Leadership News Hausa:
2025-06-16@03:26:08 GMT

Yadda Ake Hada Dublan

Published: 8th, February 2025 GMT

Yadda Ake Hada Dublan

 

Ga Yadda zaku hada:

Da farko za ku samu Tukunya sai ku zuba sukarin a ciki, ku dora shi a wuta ya narke ya yi zafi ya dan tafasa, sai ku kawo lemon tsami guda daya ku matse a ciki sai ku bar shi ya dan dahu sannan ku sauke.

Sai ku samu roba me dan girma, ku zuba fulawar a ciki sannan ku kawo Baikin Fauda ita ma ku zuba sai ku zuba dan Gishiri kadan ba da yawa ba sai ku zuba Bota idan kuma ba kuda Bota za ku iya zuba mai ku kwaba da shi, sai ku kwaba sosai ku juya shi ya juyu sosai, sannan ku samu abin murzawa ku yi ta buga shi, idan ya bugo sosai sai ku yayyankashi ku nada ku soya.

Idan kuka soya sai ku rika tsomawa a cikin sikarin da kuka dafa. Nadin Dublan kala-kala ne duk wanda kika yi ya yi idan kika kalli yadda yake.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran

A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta fitar, ta yi tir da harin na Isra’ila akan Iran tare da bayyana cewa, ya haifar da rikici a tsakanin bangarorin biyu da kuma musayar harba makamai masu linzami.

Gwamnatin ta Najeriya ta nuna bakin cikinta akan abinda ya faru, tare da kuma da yin kiran a tsagaita wutar yaki da gaggawa, da kai zuciya nesa.

Har ila yau, sanarwar ma’aikatar harkokin wajen ta Nigeria wacce kakakinta Kimiebi Imomotimi Ebienfa ya rattabawa hannu a yau Asabar,14 ga watan Yuni 2025, ta jaddada cewa; yaki ba zai maye gurbin tattaunawa ba, kuma hanyar diplomasiyya ce za ta kai ga samar da zaman lafiya mai dorewa, girmama juna da aiki da dokokin kasa da kasa.,

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 
  • Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)
  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu
  • Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)
  • Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba
  • Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran
  • Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran