Aminiya:
2025-08-02@10:19:34 GMT

Yadda rikicin shugabanci ya janyo rufe babban masallacin gari

Published: 8th, February 2025 GMT

A bayan nan ne mahukunta a Ƙaramar Hukumar Agege, a ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙaramar Hukumar Agege, Alhaji Ganiyu Kola Egunjobi suka kulle babban masallacin Hausawa na garin, biyo bayan wani rikici da ke da alaƙa da na limanci ya ɓarke a masallacin a ranar Juma’a makon jiya.

Rikicin na zuwa ne bayan rasuwar babban limamin garin Agege, Shaikh Sharif Habib Abdul-Majid, wanda ya rasu kwanaki biyu gabanin aukuwar lamarin.

Yadda Kano ke samar da madarar Naira biliyan 2.2 An dakatar da dagaci kan zargin saran maraya da adda

A wani bidiyo da ya karade kafafen sada zumunta na zamani, an ga masallata a cikin masallacin suna kai wa junansu duka, wadanda suka haɗar da ɓangarori uku.

Waɗanda suka bai wa hammatar iska sun haɗa da ɓangaren gidan limamin da ya rasu da magoya bayansu da kuma ɓangaren gidan Na’ibinsa tare da magoya bayansu, waɗanda ke fatan Na’ibin ya zama limamin gari sai kuma ɓangaren Masarautar Agege da magoya bayan masarautar.

Shaikh Mahmud Shafi’i, Baba Addini na ‘yan Arewa mazauna Legas wanda yake ɓangaren da ke fafutukar ganin Shaikh Mustapha Imam Mukhtar ya zama limamin garin Agege, domin a cewarsa shi ne Na’ibi ya shaida wa Aminiya cewa, a kan idonsa rikicin masallacin ya ɓarke a ranar Juma’a.

Ya ce bayan da Na’ibin masallacin ya shigo zai hau mumbari ne sai magoya bayan ɗan limamin masallacin da aka tanadar tare da wasu ‘yan agaji da suka hana shi hawa mumbari nan da nan kuma aka shigo da ɗan limamin da ya rasu shaikh Sharif Isma’il Habib, wanda ya ba da sallah a lokacin da ake tsaka da hayaniya.

Mustapha Imam Mukhtar ya ƙara da cewa, “an taɓa kulle masallacin ne tun a lokacin anobbar Korona, bayan barkewar wani rikici.

“Amma a wancan lokacin an cim ma yarjejeniya bayan wani zaman sulhu da sasanci da majalisar jihar ta yi da ɓangarorin da al’amarin ya shafa, inda aka cim ma daidaiton cewa, Marigayi Shaikh Sharif Habib shi ne limamin masallacin.

“Sai kuma Shaikh Mustapha Imam Mukhtar da aka tabbatar Na’ibi, kuma aka ce ba zai yiwu ɗansa ya zama Na’ibi ba, domin ba zai yiwu ba yana limanci ɗansa kuma Na’ibi ba, wanda a kan wannan yarjejeniya ake, don haka tunda liman ya rasu a ka’ida Na’ibinsa ne zai zama limamin gari, ya ci gaba da bada salla, sai dai abun takaici ne abun da ke faruwa a yanzu,” in ji shi.

Aminiya ta tuntuɓi magatakardar Masarautar Agege, Alhaji Abubakar Ali Na’ibi, wanda ya ce duk garin da ke samun ci gaba da bunƙasa ba a raba shi da irin wannan rigingimu.

Ya ce, Masarautar Agege ita ke da alhakin gudanar da al’amuran babban masallacin garin.

“Wannan al’ada haka take a ko’ina a kasar Hausa, babban masallacin gari yana ƙarƙashin kulawar masarauta ce, kuma haka abun yake a garin Agege tun fil azal, kuma Masarautar Agege ɗan marigayi limamin gari, Shaikh Sharif Isma’il Habib ta sani a matsayin Na’ibi, shi ne wanda ta naɗa Na’ibi tun da daɗewa, kuma shi ne ta sani ni a matsayin limamin gari,” in ji shi.

A wata sanarwa da Shugaban Karamar Hukumar Agege ya fitar a shafinsa na kafafen sada zumunta na zamani ya ce, matakin rufe masallacin ya zama tilas domin kare afkuwar rikici, inda ya shaida cewa, zai gayyato dukkanin ɓangarorin da ke rikici domin a zauna a teburin sulhu.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hausawa Jihar Legas Masarautar Agege Masarautar Agege Shaikh Sharif limamin gari magoya bayan

এছাড়াও পড়ুন:

Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki

Babban magatakardar kungiyar Hizbullah Sheikh Na’im Kassim ya bayyana cewa; Hizbullah tana yin aiki ne ta fuskoki biyu; na farko gwgawarmaya da HKI, sai kuma a fagen Siyasa a cikin gida.

Shugaban kungiyar ta Hizbullah wanda ya gabatar da jawbai a jiya domin girmama babban kwamandan kungiyar Hizbullah Shahid Sayyid Fu’ad Shukr ya ce; An zabi shugaban kasa Joseph Aun ne bayan da aka dauki shekaru ba tare da shugaban kasa ba a kasar. Kuma kungiyar gwagwarmaya ta tabbatar da cewa ginshiki ne a fagen siyasa, wacce ta saukaka yadda aka zabi shugaban kasar da kafa gwamnati.”

Har ila yau Sheikh Naim Kassim ya yi bayani akan yadda gwagwarmaya ta kafu a cikin kasar Lebanon a matsayin mayar da martani ga mamayar HKI, ta kuma cike gibin da sojoji su ka bari, da a karshe a 2000 ta kori HKI daga cikin Lebanon.

Sheik Na’im Kassim ya kuma ce; Gwgawarmaya wani nauyi ne da rataya akan kowa, ba wai zabi ba ne,kuma lokacin da aka yi aiki a tsakanin gwgawarmaya, soja da al’umma an cimma nasarori masu yawan gaske.

Babban  magatakardar kungiyar ta Hizbullah sheik Na’im Kassim ya kuma ce; Batun makaman dake hannun kungiyar Hizbullah wani batu ne da ya shafi cikin gidan kasar Lebanon, don haka ba shi da wata alaka da HKI.”

Akan batun kwance damarar yakin kungiyar ta Hizbullah, Sheikh Na’im Kassim ya ce, duk wanda yake son ganin hakan ta faru, to yana yi wa Isra’ila aiki ne.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata July 31, 2025 Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila July 31, 2025 Kasar Iran Ta Bayyana Gushewar Hasashen Raunin Karfin Sojinta Kuma Ba Zai Dawo Ba July 31, 2025 Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine July 31, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku   July 31, 2025 Qolibaf: Barin HKI Ta Yi Abinda Taga Dama Ne Yana Karfafa Mata Giwa July 30, 2025 Yunwa Ta Kashe Karin Falasdinawa 7 A Gaza July 30, 2025 Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa July 30, 2025 Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah July 30, 2025 Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku July 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda binciken zargin tallafa wa Boko Haram ke tafiyar hawainiya a Majalisa
  • Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa
  • 2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa
  • Limamin Sallar Juma’a Ya Ce; Iran Zata Mayar Da Isra’ila Kufai Idan Ta Sake Kai Hari Kan Kasarta
  • Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6
  • Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki
  • Dalilan Da Suka Sa Canada Ta Goyi Bayan Kafa Kasar Falasɗinu
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  •  Yahudawa ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Cikin Masallacin Kudus
  • Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu