Aminiya:
2025-06-15@13:15:18 GMT

Yadda rikicin shugabanci ya janyo rufe babban masallacin gari

Published: 8th, February 2025 GMT

A bayan nan ne mahukunta a Ƙaramar Hukumar Agege, a ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙaramar Hukumar Agege, Alhaji Ganiyu Kola Egunjobi suka kulle babban masallacin Hausawa na garin, biyo bayan wani rikici da ke da alaƙa da na limanci ya ɓarke a masallacin a ranar Juma’a makon jiya.

Rikicin na zuwa ne bayan rasuwar babban limamin garin Agege, Shaikh Sharif Habib Abdul-Majid, wanda ya rasu kwanaki biyu gabanin aukuwar lamarin.

Yadda Kano ke samar da madarar Naira biliyan 2.2 An dakatar da dagaci kan zargin saran maraya da adda

A wani bidiyo da ya karade kafafen sada zumunta na zamani, an ga masallata a cikin masallacin suna kai wa junansu duka, wadanda suka haɗar da ɓangarori uku.

Waɗanda suka bai wa hammatar iska sun haɗa da ɓangaren gidan limamin da ya rasu da magoya bayansu da kuma ɓangaren gidan Na’ibinsa tare da magoya bayansu, waɗanda ke fatan Na’ibin ya zama limamin gari sai kuma ɓangaren Masarautar Agege da magoya bayan masarautar.

Shaikh Mahmud Shafi’i, Baba Addini na ‘yan Arewa mazauna Legas wanda yake ɓangaren da ke fafutukar ganin Shaikh Mustapha Imam Mukhtar ya zama limamin garin Agege, domin a cewarsa shi ne Na’ibi ya shaida wa Aminiya cewa, a kan idonsa rikicin masallacin ya ɓarke a ranar Juma’a.

Ya ce bayan da Na’ibin masallacin ya shigo zai hau mumbari ne sai magoya bayan ɗan limamin masallacin da aka tanadar tare da wasu ‘yan agaji da suka hana shi hawa mumbari nan da nan kuma aka shigo da ɗan limamin da ya rasu shaikh Sharif Isma’il Habib, wanda ya ba da sallah a lokacin da ake tsaka da hayaniya.

Mustapha Imam Mukhtar ya ƙara da cewa, “an taɓa kulle masallacin ne tun a lokacin anobbar Korona, bayan barkewar wani rikici.

“Amma a wancan lokacin an cim ma yarjejeniya bayan wani zaman sulhu da sasanci da majalisar jihar ta yi da ɓangarorin da al’amarin ya shafa, inda aka cim ma daidaiton cewa, Marigayi Shaikh Sharif Habib shi ne limamin masallacin.

“Sai kuma Shaikh Mustapha Imam Mukhtar da aka tabbatar Na’ibi, kuma aka ce ba zai yiwu ɗansa ya zama Na’ibi ba, domin ba zai yiwu ba yana limanci ɗansa kuma Na’ibi ba, wanda a kan wannan yarjejeniya ake, don haka tunda liman ya rasu a ka’ida Na’ibinsa ne zai zama limamin gari, ya ci gaba da bada salla, sai dai abun takaici ne abun da ke faruwa a yanzu,” in ji shi.

Aminiya ta tuntuɓi magatakardar Masarautar Agege, Alhaji Abubakar Ali Na’ibi, wanda ya ce duk garin da ke samun ci gaba da bunƙasa ba a raba shi da irin wannan rigingimu.

Ya ce, Masarautar Agege ita ke da alhakin gudanar da al’amuran babban masallacin garin.

“Wannan al’ada haka take a ko’ina a kasar Hausa, babban masallacin gari yana ƙarƙashin kulawar masarauta ce, kuma haka abun yake a garin Agege tun fil azal, kuma Masarautar Agege ɗan marigayi limamin gari, Shaikh Sharif Isma’il Habib ta sani a matsayin Na’ibi, shi ne wanda ta naɗa Na’ibi tun da daɗewa, kuma shi ne ta sani ni a matsayin limamin gari,” in ji shi.

A wata sanarwa da Shugaban Karamar Hukumar Agege ya fitar a shafinsa na kafafen sada zumunta na zamani ya ce, matakin rufe masallacin ya zama tilas domin kare afkuwar rikici, inda ya shaida cewa, zai gayyato dukkanin ɓangarorin da ke rikici domin a zauna a teburin sulhu.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hausawa Jihar Legas Masarautar Agege Masarautar Agege Shaikh Sharif limamin gari magoya bayan

এছাড়াও পড়ুন:

Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta roƙi ƙasashen Isra’ila da Iran da su daina rikici, su zauna lafiya su sasanta tsakaninsu. 

A wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Waje ta fitar, ta bayyana damuwa kan yadda rikicin ke ƙara ta’azzara, inda ta nemi ɓangarorin biyu da su kai zuciya nesa don samar da zaman lafiya a duniya baki ɗaya.

Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung

Sanarwar ta ce faɗa da ramuwar gayya na jefa rayukan fararen hula cikin hatsari, kuma yana iya haddasa rikici mai muni a yankin Gabas ta Tsakiya, wanda hakan zai iya barazana ga tsaron duniya da kuma ci gaban tattalin arziƙi dunuya.

“Mu a matsayimmu na ƙasa mai son zaman lafiya, muna roƙon ƙasashen da ke rikici da su zauna su tattauna maimakon su ci gaba da faɗa.”

Gwamnatin Tarayya ta kuma yi kira ga ƙasashen duniya, musamman Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya, da su ɗauki matakai don hana yaɗuwar rikicin da kuma samo hanyar warware matsalar.

Sanarwar ta ƙara da cewa amfani da ƙarfin soji ba shi da amfani matuƙa, domin faɗa ba zai kawo sauƙi ba.

Najeriya ta ce a shirye ta ke ta bayar da taimako domin hana yaɗuwar rikicin da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu
  • Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)
  • Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
  • An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari
  • Hamas : Ziyarar ministan Isra’ila Ben-Gvir a masallacin al-Aqsa kan iya tayar da yakin addini