MDD Ta Yi Gargadi Akan Halin Da Ake Ciki A DRC
Published: 6th, February 2025 GMT
Kungiyar M 23 mai samun goyon bayan Rwanda ta kara samun gindin zama a gabashin kasar DRC, duk da cewa ta sanar da tsagaita wutar yaki ta gefe daya a jiya Laraba.
Mayakan na M 23 sun sanar da kame babban binin gundumar Bukavu.
Wani jami’in MDD wanda ya isa garin Goma ya bayyana cewa, Da akwai yiyuwar barkewar wani sabon rikici.
MDD ta ce har yanzu ana ci gaba da yaki tsakanin sojojin gwamnati da kuma mayakin na kungiyar M 23.
Garin Goma da mayakan na M 23 su ka kwace iko da shi, yana da ma’adanai kwance a kasansa da aka yi kirdadon cewa kudadensa sun kai na biliyoyin daloli.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
HKI Tana Amfani Yunwa A Matsayin Makamin Yaki A Kan Falasdinawa A Gaza
Wakilin falasdinawa a kutun kasa da kasa ta ICJ da ke birnin Haque na kasar Nerthelands yace HKI tana amfani da hana kayakin agaji daga ciki har da abinci shiga gaza a matsayin makami kan Falasdinawa don kashesu.
Tashar talabijib ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Ammar Hijazi jakadan kasar Faladinu a cibiyoyin MDD a kasashen Turai yana fadar haka a gaban alkalai a kotun ta ICJ a jiya litinin.
Ya ce HKI tana kisa ta sama da makamai, sannan tana kisa ta kasa da yunwa banda haka tana ci gaba da korar Falasdinawa daga yankin yamma da kogin Jordan tun fiye da watanni 3 da sua habata.
Kutun ta bude wannan zaman ne bisa bukatar MDD ta shekara ta 2024 na bincike don tabbatar da cewa HKI tana amfani yunwaa a matsayin makami a Gaza. Ammar Hijazi ya kara da cewa banda wannan babban kotun HKI tana goyon bayan amfani da yunwa a matsayin makami a gaza tun fiye da watanni 2 da suka gabata.
Wasu lauyoyi daga kasashe daban–daban wadanda suka hada da Nerthlands da Afirka ta kudu duk sun yi magana sun kuma yi allawadai da HKI kan abinda take aikatawa a Gaza.