HausaTv:
2025-06-15@22:41:14 GMT

MDD Ta Yi Gargadi Akan Halin Da Ake Ciki A DRC

Published: 6th, February 2025 GMT

Kungiyar M 23 mai samun goyon bayan Rwanda ta kara samun gindin zama  a gabashin kasar DRC, duk da cewa ta sanar da tsagaita wutar yaki ta gefe daya a jiya Laraba.

Mayakan na M 23 sun sanar da kame babban binin gundumar Bukavu.

Wani jami’in MDD wanda ya isa garin Goma ya bayyana cewa, Da akwai  yiyuwar barkewar wani sabon rikici.

 MDD ta ce har yanzu ana ci gaba da yaki tsakanin sojojin gwamnati da kuma  mayakin na kungiyar M 23.

Garin Goma da mayakan na M 23 su ka  kwace iko da shi, yana da  ma’adanai kwance a kasansa da aka yi  kirdadon cewa kudadensa sun kai na biliyoyin daloli.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran

Isra’ila ta kaddamar da hare hare kan wasu gine-gine da cibiyoyi a sassa daban daban na Iran ciki har da Tehran babban birni a cikin daren jiya wayewar wannan safiya ta Juma’a.

Kafofin yada labarai na Iran sun ce akwai mata da yara da dama daga cikin wadanda suka yi shahada a hare-haren.

An kuma bayar da rahoton kai hari a wurare a Natanz, Khorramabad, da Khondab, da dai sauransu.

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce harin da Isra’ila ta kai wa Iran zai kai tsawon kwanaki idab akwai bukatar hakan.

“Za a ci gaba da gudanar da wannan aiki na tsawon kwanaki kamar yadda ake tsara don kawar da wannan barazanar,” in ji Netanyahu a cikin wata sanarwa ta bidiyo.

Hare-haren da sojojin gwamnatin sahyoniyawan suka kai kan Tehran ya yi sanadiyar shahadar wasu fitattun masana kimiyyar nukiliya na Iran, Mohammad Mahdi Tehranchi da Fereydoon Abbasi, dama wasu fararen hula.

Tehranchi shi ne shugaban jami’ar Azad ta Musulunci ta Iran.

Fereydoon Abbasi ya kasance tsohon shugaban hukumar makamashin nukiliya ta Iran.

An dakatar da zirga-zirgar jiragai a filin jirgin saman Imam Khumaini na Tehran.

Harin ya zo ne kwanaki biyu gabanin wani sabon zagaye na shawarwarin nukiliyar Iran da Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Kasar Iran Sun Ce Bazasu Dakatar Da Yaki ba Har Zuwa Samun Nasara A kan HKI
  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Aike Da Sako Ga Al’ummar Iran Bayan Harin Da Iran Ta Fuskanta
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci
  • Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Rundinar IRGC, ta sanar da shahadar babban kwamandanta Manjo Janar Hossein Salami a harin ta’addancin Isra’ila
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran