Isra’ila Ta Umurci Sojoji Su Shirya Tsarin Fitar Da Faladinawa Dake So Daga Gaza
Published: 6th, February 2025 GMT
Ministan tsaron Isra’ila, Isra’ila Katz ya umarci sojojin gwamnatin kasar da su shirya wani shiri na “ficewar” Falasdinawa daga zirin Gaza.
Umarnin Katz ya biyo bayan shawarar Shugaba Donald Trump na tilastawa Falasdinawa Gaza barin zirin da kuma sanya Amurka ta mamaye yankin da yaki ya lalata.
“Na umurci IDF da su shirya wani shiri don ba da damar ficewa na radin kan mazauna Gaza,” in ji kakakin na Isra’ila a cikin wata sanarwa.
Katz ya bayyana cewa ya fadawa sojojin Isra’ila da su yi shirin da “zai ba da damar duk wani mazaunin Gaza da ke son barin yankin zuwa, ga duk wata kasa da yake son karba.”
Ministan tsaron Isra’ila ya kara da cewa “Tsarin zai hada da zabin fita ta kasa, da kuma shirye-shirye na musamman na jiragan sama da kuma na ruwa.”
Katz ya ce yana maraba da “tsarin da Trump ya dauka, wanda zai iya baiwa wani kaso mai yawa na al’ummar Gaza damar yin kaura zuwa wurare daban-daban na duniya.”
A wani labarin kuma kungiyar Hamas ta bukaci da a gudanar da taron gaggawa na kasashen Larabawa domin mayar da martani ga shawarar da shugaba Donald Trump ya gabatar na mamaye yankin Falasdinu da kuma korar al’ummar kasar.
A cikin wata sanarwa da kakakin Hamas Hazem Qassem ya fitar, ya ce “Muna kira da a gudanar da taron gaggawa na kasashen Larabawa don tunkarar shirin korar Palasdinawa daga Gaza, inda ya bukaci kasashen Larabawa da su bijirewa matsin lambar Trump, su kuma jajirce,” yayin da ya yi kira ga kungiyoyin kasa da kasa da su dauki kwararan matakai kan shirin na Trump.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Al-Shara Ya Ki Abincikewa Da Tsarin Tarayya Wanda Kurdawan Kasar Siriya Suke Bukata
Shugaban kasar Siriya ya ki amincewa da bukatar kurdawan kasar daga dakarun Democradiyyan kurdawa wato (SDF), na samar da tsarin tarayya a kasar bayan kifar da gwanatin Basshar Al-Asab.
Jaridar The Nation ta nakalto shuga Al-Ahmad Sharaa yana fadar haka a jiya Lahadi ya kuma kara da cewa tsarin tarayyar barazana ce ga hadin kan kasar ta Siriya sannan tsarin tarayya ya sabawa yarjeniyar da aka kulla da kurdawan a baya-bayan nan.
A wani taron da suka gabatar a makon da ya gabata, jam’iyyar kurdawan kasar ta Siriya (SDC) ta fadawa “ The National ” bayan taron kan cewa suna bukatar tsarin tarayyar a kasar Siriya don shi ne kadai zai tabbatar da hakkinsu a kasar.
A cikin watan maris da ya gabata ne shugaba Al-Sharaa na kasar Syriya ya rattaba hannu a kan wata yarjeniya da shugaban dakarun kurdawan kasar Siriya SDF Mazlum Abdi dangane da hade dakarunsa da sojojin kasar Siriya, sannan yace tsarin tarayya ya sabawa wannan yarjeniyar.