Isra’ila Ta Umurci Sojoji Su Shirya Tsarin Fitar Da Faladinawa Dake So Daga Gaza
Published: 6th, February 2025 GMT
Ministan tsaron Isra’ila, Isra’ila Katz ya umarci sojojin gwamnatin kasar da su shirya wani shiri na “ficewar” Falasdinawa daga zirin Gaza.
Umarnin Katz ya biyo bayan shawarar Shugaba Donald Trump na tilastawa Falasdinawa Gaza barin zirin da kuma sanya Amurka ta mamaye yankin da yaki ya lalata.
“Na umurci IDF da su shirya wani shiri don ba da damar ficewa na radin kan mazauna Gaza,” in ji kakakin na Isra’ila a cikin wata sanarwa.
Katz ya bayyana cewa ya fadawa sojojin Isra’ila da su yi shirin da “zai ba da damar duk wani mazaunin Gaza da ke son barin yankin zuwa, ga duk wata kasa da yake son karba.”
Ministan tsaron Isra’ila ya kara da cewa “Tsarin zai hada da zabin fita ta kasa, da kuma shirye-shirye na musamman na jiragan sama da kuma na ruwa.”
Katz ya ce yana maraba da “tsarin da Trump ya dauka, wanda zai iya baiwa wani kaso mai yawa na al’ummar Gaza damar yin kaura zuwa wurare daban-daban na duniya.”
A wani labarin kuma kungiyar Hamas ta bukaci da a gudanar da taron gaggawa na kasashen Larabawa domin mayar da martani ga shawarar da shugaba Donald Trump ya gabatar na mamaye yankin Falasdinu da kuma korar al’ummar kasar.
A cikin wata sanarwa da kakakin Hamas Hazem Qassem ya fitar, ya ce “Muna kira da a gudanar da taron gaggawa na kasashen Larabawa don tunkarar shirin korar Palasdinawa daga Gaza, inda ya bukaci kasashen Larabawa da su bijirewa matsin lambar Trump, su kuma jajirce,” yayin da ya yi kira ga kungiyoyin kasa da kasa da su dauki kwararan matakai kan shirin na Trump.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)
Shugaban aksar Iran, Massoud Pezeshkian, ya bayyana cewa martanin sojojin kasarsa ga Isra’ila zai zama mafi muni idan hare-haren Isra’ilar suka ci gaba.
A wata tattaunawa ta wayar tarho da firaministan Pakistan Shehbaz Sharif, shugaban kasar Iran Massoud Pezeshkian ya tabbatar da cewa dakarun gwamnatin Jamhuriyar Musulunci ta Iran za su dauki kwararan matakan mayar da martani mai tsauri idan har gwamnatin Isra’ila ta ci gaba da kai farmaki kan Iran.
“Masu da’awar kare hakkin bil’adama ba wai kawai suna goyon bayan zaluncin gwamnatin sahyoniyawa ba ne, har ma suna karfafa mata gwiwar aikata wadannan munanan ayyuka ta hanyar ba ta makamai da kayan aiki,” in ji shi.
Mr. Pezeshkian ya kara da cewa gwamnatin Isra’ila da ke samun goyon bayan Amurka da kasashen yammacin Turai ta sabawa dukkanin dokokin kasa da kasa.
A nasa bangaren, firaministan Pakistan ya bayyana goyon bayan kasarsa ga al’ummar iran, yana mai yin Allah wadai da keta hurumin kasar Iran da ‘yancinta, wanda ya zama cin zarafi ga dokokin kasa da kasa da kuma kundin tsarin mulkin MDD.
Sharif ya sake jaddada cewa Iran na da cikakken ‘yancin kare kanta a karkashin doka ta 51 na kundin tsarin mulkin MDD inda ya bayyana fatan ganin an dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.