’Yan sanda sun kama baƙin haure 165 a Kebbi
Published: 5th, February 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kebbi, ta kama wasu mutum 165 da suka shigo Najeriya ba tare da izini ba.
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, Nafi’u Abubakar, ya ce an kama mutanen ne a Birnin Kebbi.
Gobara ta yi ajalin almajirai 17 a Zamfara Tinubu ya ƙara kasafin kuɗin 2025 zuwa N54.2trnYa ce 35 daga cikinsu ’yan asalin ƙasar Burkina Faso ne, yayin da 11 ’yan asalin Jamhuriyar Benin ne.
Akwai kuma mutum biyar daga Nijar, huɗu daga Mali, sai mutum 110 ’yan ƙasar Ivory Coast.
Ya ce mutanen ba su da takardun izinin shigowa Najeriya kuma an same su da aikata damfara.
Rundunar ta bayyana cewa an miƙa su ga Hukumar Shige da Fice ta Ƙasa da ke Jihar Kebbi, domin gudanar da bincike da kuma ɗaukar matakin da ya dace.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Najeriya Rashin Izini
এছাড়াও পড়ুন:
Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
Duk da cewa, yanayin zafi ya yawaita a kasar ta Saudiyya, yayin gudanar da aikin Hajjin 2025, koda-yake; akasarin wadanda suka mutu daga Nijeriyar tsofaffi ne.
Rasuwar farko da aka sanar ta wani Alhaji ce daga Jihar Oyo, Alhaji Sulaimon Hamzat, wanda ya rasu a ranar 17 ga Mayun 2025 a kasar ta Saudiyya.
Na biye da shi kuma daga Jihar Abiya ne, mai suna Alhaji Saleh, Shugaban Kasuwar Shanu ta Lokpanta, wanda ya rasu a garin Makka a daren ranar Litinin 26 ga watan Mayun 2025.
Bayan haka kuma, sai wata Hajiya mai shekaru 75 daga Jattu Uzairue a Karamar Hukumar Etsako ta yamma da ke Jihar Edo, Adizatu Dazumi, wadda ta mutu a ranar Litinin 26 ga Mayun 2025, bayan gajeriyar rashin lafiya.
An samu rahoton cewa, Dazumi ta kamu da rashin lafiya jim kadan bayan kammala dawafi, inda aka garzaya ta ita zuwa asibitin Sarki Fahad da ke Makka a ranar Lahadi, washegari kuma ta mutu.
Haka zalika, wata Hajiya daga Jihar Filato ta rasu a birnin Makka da ke Saudiyya, yayin gudanar da wannan aiki Hajjin 2025.
Marigayiyar, mai suna Hajiya Jamila Muhammad, ta rasu ne sakamakon cutar Siga da ke fama da shi a asibitin Sarki Abdul’aziz da ke birnin Makka.
Kwana daya kafin fara aikin Hajjin 2025, wani Alhaji daga Jihar Kano mai suna Shu’aibu Jibrin, ya rasu a garin Makka.
Haka nan kuma, wani Alhajin Nijeriya ya rasu a filin Arfa.
A cewar Shugaban Hukumar Alhazai ta Nijeriya, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, “Mun samu labari mara dadi cewa; mun rasa mahajjatanmu a yau Arfat, dayan kuma ya rasu kafin mu bar Makka,” in ji shi.
Ya kuma ce, mutuwar Alhazan daga Allah ne; inda ya kawar da rade-radin da ake yin a cewa, zafin rana ne ya haddasa su.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp