Aminiya:
2025-05-01@06:25:00 GMT

’Yan sanda sun kama baƙin haure 165 a Kebbi

Published: 5th, February 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kebbi, ta kama wasu mutum 165 da suka shigo Najeriya ba tare da izini ba.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, Nafi’u Abubakar, ya ce an kama mutanen ne a Birnin Kebbi.

Gobara ta yi ajalin almajirai 17 a Zamfara Tinubu ya ƙara kasafin kuɗin 2025 zuwa N54.2trn

Ya ce 35 daga cikinsu ’yan asalin ƙasar Burkina Faso ne, yayin da 11 ’yan asalin Jamhuriyar Benin ne.

Akwai kuma mutum biyar daga Nijar, huɗu daga Mali, sai mutum 110 ’yan ƙasar Ivory Coast.

Ya ce mutanen ba su da takardun izinin shigowa Najeriya kuma an same su da aikata damfara.

Rundunar ta bayyana cewa an miƙa su ga Hukumar Shige da Fice ta Ƙasa da ke Jihar Kebbi, domin gudanar da bincike da kuma ɗaukar matakin da ya dace.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Najeriya Rashin Izini

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasu

Allah Ya yi wa Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Muslunci a Najeriya, Sheikh Abdul Rasheed Hadiyatullah, rasuwa.

Babban Mufti na ƙasar Yarbawa, Sheikh Daood Imran Molaasan, ne ya sanar da rasuwar Sheikh Abdul Rasheed Hadiyatullah a cikin wata sanarwa da ya sanya hannu a kai a daren Litinin.

Sai dai bai bayar da cikakken bayani game da inda Sheikh Hadiyatullah ya rasu ko kuma lokacin da hakan ya faru ba.

Sheikh Molaasan ya bayyana cewa rasuwar marigayi Sheikh Hadiyatullah ta bar giɓi mai wuyar cikewa a shugabancin Musulunci na ƙasar.

Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya

“An haife shi a garin Iwo a Jihar Osun kuma an san shi da dabi’u  Musulunci. Sheikh Hadiyatullah ya kasance fitaccen malamin Musulunci kuma masanin shari’a, wanda an san shi da ƙoƙarinsa na neman a aiwatar da Shari’a Musulunci a tsarin mulkin Najeriya, tattaunawa tsakanin addinai, da zaman lafiya a tsakanin al’ummomin Najeriya masu bambancin addini.

“Ya yi aiki a matsayin Shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci na tsawon shekaru, inda ya jagorance ta a lokutan ƙalubalen zamantakewa da ci gaba.

“Sheikh Hadiyatullah ya fara karatun addinin Musulunci a wurin malaman gida kafin ya ci gaba da karatunsa a ƙasashen waje.

“Ya samu girmamawa a faɗin Najeriya da ma wajenta saboda zurfin ilminsa a fannin fiƙihun Musulunci da kuma salon shugabancinsa mai nutsuwa da tsayin daka kan akida,” kamar yadda Molaasan ya bayyana.

Ya kuma yi addu’ar Allah ya gafarta wa Sheikh Hadiyatullah ya kuma ba shi Aljannatul Firdaus.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  • DAGA LARABA: Asarar Da Hausawa Ke Tafkawa Sakamakon Bacewar Tatsuniya
  • HOTUNA: Yadda aka dawo da ’yan Najeriya 203 daga Libya
  • Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasu
  • Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu
  • NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya
  • Jihar Kebbi Ta Kammala Shirye-shiryen Aikin Hajjin 2025
  • Mutanen da talauci ya yi wa katutu zai ƙaru a Nijeriya — Bankin Duniya
  • Ƴansanda Sun Kama Ƴan Daba 33 A Kano