Aminiya:
2025-08-02@00:32:58 GMT

Kungiyar NLC ta kira zanga-zanga kan ƙarin kuɗin waya

Published: 30th, January 2025 GMT

Kungiyar Ƙwadago ta Ƙasa (NLC) ta kira zanga-zangar adawa da ƙarin data da kiran waya a Najeriya.

NLC ta umarci rassanta na jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya da su shirya domin fara zanga-zangar daga ranar Takara 4 ga watan Fabrairu mai kamawa.

Ta bayyana cewa manufar zanga-zangar ita ce ganin an janye karin kashi 50% da aka yi wa kuɗin kiran waya da na data, da kuma adawa da tsadar rayuwa wadda ta jefa ’yan Najeriya cikin tasku.

Shugaban ƙungiyar, Joe Ajaero, ya bayyana cewa zanga-zangar zai zama gargaɗi ga shugabanni kan dore wa al’umma abin da bai dace ba sa rashin adalci.

“Wannan gangami zai yaƙi ƙare-ƙaren ganin dama rashin adalci da aka yi na man fetur da wutar lantarki da hauhawan farashin kaya alhali an bar mutane da albashin N70,000 wanda bai taka kara ya karya ba,” in ji shi.

Ya ci gaba da cewa, duk rassan NLC da ƙungiyoyin fararen hula da dangoginsu a shirye suke su shiga wanan yakjn aiki.

Don haka ya buƙaci hukumar sadarwa ta ƙasa da majalisar dokoki ta kasa su tattauna da masu ruwa da tsaki domin samun maslaha kan ƙarin kuɗin da suka tsara.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yajin aiki zanga zangar

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Jihar Sokoto ta umarci Kwamishinan harkokin makamashi da albarkatun man Fetur, Hon. Sanusi Danfulani, da ya bayyana a gabanta ranar Talata, 5 ga watan Agusta, saboda gazawarsa wajen halartar ziyarar duba aiki da kwamitin majalisar mai kula da kimiyya da fasaha ya gudanar.

Ziyarar da aka shirya a ranar Alhamis ta sami tsaiko sakamakon rashin halartar Danfulani da wasu manyan jami’an ma’aikatarsa, lamarin da shugaban kwamitin, Awaisu Aliyu, ya bayyana a matsayin “wulakanci da sakaci da aiki da ga rashin mutunta majalisar dokoki.”

Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Aliyu ya ce, “An aika musu da sanarwa cikin lokaci game da ziyarar, amma babu wani jami’i daga ma’aikatar da ya halarta, sannan babu wani bayani na rashin zuwa daga gare su.”

Ya ƙara da cewa irin wannan sakaci yana tauye ikon da kundin tsarin mulki ya bai wa majalisar wajen gudanar da aikinta na sa ido. Don haka, ya umurci Danfulani da ya halarci zaman majalisar a ranar 5 ga Agusta ko kuma ya fuskanci hukunci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili
  • GORON JUMA’A 01-07-2025
  • Kungiyar AU Ta Yi Watsi Da Kafa Gwamnatin Adawa Da Kungiyar RSF Ta Yi A Sudan
  • Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki
  • Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kura
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
  • Rashin Nasarar DPP A Zagayen Farko Na Kuri’ar Kiranye Ya Nuna Rashin Amincewar Al’ummar Taiwan Da Salon Mulkin Jami’yyar
  • Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana