Aminiya:
2025-06-15@01:49:55 GMT

Sojoji sun ƙwato tarin makamai a Zamfara

Published: 28th, January 2025 GMT

Dakarun rundunar Operation Fansar Yamma sun ce sun ƙwato tarin makamai a Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda na Jihar Zamfara.

Dakarun tare da haɗin gwiwar jami’an tsaron farin kaya (DSS), sun kai samamen ne bayan samun bayanan sirri kan masu safarar makamai daga Jamhuriyar Nijar zuwa Najeriya.

Tankar mai ta sake fashewa a Neja Jadawalin Gasar AFCON 2025 da za a fafata a Morocco

Wata sanarwa da jami’in yaɗa labaran rundunar, Laftanar-Kanal Abubakar Abdullahi ya fitar, ya ce sun ƙaddamar da farmaki ranar 27 ga watan Janairun 2025, abin da ya kai ga ƙwato makaman kan hanyar Namoda zuwa Zurmi.

Ya ce waɗanda ake zargin sun tsere zuwa cikin daji tare da barin motarsu bayan artabu da sojoji.

Kanal Abubakar ya ce bayan binciken da suka yi a cikin motar, sun gano makamai da dama da suka haɗa da bindigar AK-47 guda tara da harsasai daban-daban.

A ɗaya gefen, dakarun sun ce sun baza koma domin cafke ƙasurgumin ɗan bindigar nan Bello Turji wanda ake nema ruwa a-jallo.

Bayanai sun ce Turji na ci gaba da guje-guje da sojoji daga maɓoya zuwa maɓoya.

Dakarun sun tabbatar da cewa suna aiki tuƙuru domin kama Turji da zummar dawo da zaman lafiya a al’ummomin da suka addaba da hare-hare.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: dakaru Jihar Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

HKI Ta Rufe Filin Saukar Jiragen Sama Na Ben Gorion Tare Da Dauke Jiragenta  Zuwa Waje

Mai magana da yawun hukumar da take kula da filin saukar jiragen sama ta Ben Gorion ta sanar a yau Asabar cewa an rufe filin saukar jiragen saman har zuwa wani lokaci a nan gaba, bayan da aka dauke dukkanin jiragen sama zuwa kasashen Cyprus, Greece da kuma Amurka.

Mai Magana da yawun hukumar filin saukar jiragen saman na Ben Gorion  Lisa Daiper ta bayyana ce; Babu wani lokaci takamaimai da aka tsayar domin sake bude filin saukar jiragen saman na Ben Gorion.”

 A gefe daya jaridar “Maariv’ ta bayyana cewa; An dauke dukkanin jiragen sama zuwa filayen  jiragen saman a kasashen turai.

Haka nan kuma ta kara da cewa; An dauki 14 daga cikin jiragen saman na HKI zuwa filin saukar jiragen saman a Laranka da Papus dake tsibirin Cyprus da su ne filayen jiragen sama na nahiyar turai mafi kusa da HKI.

Su kuwa jiragen da shugabannin ‘yan sahayoniya suke shiga an kai su ne zuwa filin jirgin sana na birnin Athenia na kasar Girka, wasu kuwa zuwa kasashen Bulgari da Faransa.

Dauke jiragen na ‘yan sahayoniya dai ya zo ne saboda tsoron kar makamai masu linzami na Iran su isa gare su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • HKI Ta Rufe Filin Saukar Jiragen Sama Na Ben Gorion Tare Da Dauke Jiragenta  Zuwa Waje
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Kakkabo Jiragen Yakin Isra’ila Biyu Kirar F-35
  • Iran, ta yi wa Isra’ila ruwan makamai masu linzami
  • An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
  • Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane