Kasar Sin ta yi nasarar harba sabon rukunin taurarin dan adam mai da’ira a kusa da doron kasa, daga cibiyar harba tauraron dan Adam ta Taiyuan dake lardin Shanxi na arewacin kasar Sin.

An harba rukunin wanda shi ne irinsa na 4 da ya kunshi taurari masu samar da sadarwar intanet da misalin karfe 4:45 na sanyin safiyar yau Juma’a agogon Beijing, ta hanyar amfani da rokar Long March-6 da aka sakewa fasali.

Kuma dukkan taurarin sun shiga da’irarsu cikin nasara.

Wannan shi ne karo na 580 da aka yi amfani da dangin rokar Long March wajen gudanar da irin wannan aiki. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Ba’a Rufe Kofar Diblomasiyya Ba, Matukar HKI Ta Dakatar Da Kaiwa Kasar HKI

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ya bayyaana cewa kasarsa bata rufe kofar diblomasiyya dangane da shirinta na makamashin Nukliya ba, matukar HKI zata dakatar da hare-haren da take kaiwa kasar.

Kamfanin dillancin  labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka a yau Lahadi a taron yan jaridun da ya kira a birnin Tehran. Ya kuma kara da cewa Iran tana son ta ci gaba da shirinta na makamashin Nukliya ta zaman lafiya ta hanyar diblomasiyya idan an bata damar yin haka.

Ministan ya ce ikidar JMI ne warware dukkan matsaloli da farko ta hanyar Diblomasiyya, da kuma tattaunawa amma ba zamu taba amincewa  wani ya hanamu hakkimu na mallakar makamashi nukliya ta zaman lafiya ba. Kuma mun bayyana cewa a shirye muke a gudanar da bincike a ayyukammu. Sojojin Iran sun cilla wasu sabbin hare-hare a kan HKI a yau Lahadi da rana.

Yakin da HKI ta fara a safiyar jumma’an da ta gabata, mai kuma samun goyon bayan Amurka, don tilsatawa Iran amincewa da sharuddanta na shirin Iran na makamashin nukliya ne.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Buni ya bai wa manoma 1,000 tallafin aikin gona
  • Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575
  • Matatar man Isra’ila ta daina aiki bayan sabon harin Iran
  • Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga
  • Sin Ta Fatattaki Laifukan Zamba Ta Shafin Intanet 294,000 A Bara
  • Sabon harin Iran ya hallaka mana mutum 8 – Isra’ila
  • Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Ba’a Rufe Kofar Diblomasiyya Ba, Matukar HKI Ta Dakatar Da Kaiwa Kasar HKI
  • Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Bayyana Sabon Salon Mayar Da Martani Kan Isra’ila
  • Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila