Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ben Gurion Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila
Published: 5th, June 2025 GMT
Sojojin Yemen sun kai hare-hare kan filin jirgin saman Lod da ke Jaffa da aka mamaya da jiragen sama biyu marasa matuka ciki
Sojojin Yemen sun sanar da kai wani farmakin soji kan tashar jirgin saman Lod da ke yankin Jaffa da aka mamaye, domin jaddada goyon baya ga al’ummar Falastinu da ake zalunta da kuma nuna tsananin Rashin amincewa da kisan kiyashin da makiya yahudawan sahayoniyya suke yi kan ‘yan uwansu a zirin Gaza.
Rundunar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a yau, inda ta ce farmakin da rundunar sojin saman Yemen ta kai da jiragen saman yaki marasa matuka ciki kirar Yaffa guda biyu, ya samu nasarar cimma burin da ake bukata.
Rundunar sojin ta yi nuni da cewa: A daidai lokacin da mahajjatan dakin Allah suke shirin tsayuwa a Arafat, suna tasbihi da gode wa Allah, ana ci gaba da zubar da jinin ‘yan uwansu a Gaza, ba tare da wani mataimaki ko mai ceto daga al’ummar musulmi ba, duk kuwa da irin karfin da za a iya kawo karshen wannan kisan kiyashi, wanda duniya ba ta taba ganin irinsa ba.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Musanta Zargin Amurka Kan Cewa Kungiyoyi Masu Fada Ha HKI Suna Daukar Umurni Daga Wajenta Ne
Jakadan kasar Iran a MDD Amir Sa’eid Iravani ya musanta zargin kasar Amurka na cewa falasdinawa dauke da makamai a Gaza suna aiki ne tare da umurnin Iran. A kuma dukkan yankunan da HKI take mamaye da su a kasar Falasdinu da ta mamaye.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ya nakalto Iran vani yana cewa Amurka ta dorawa iran wannan zargin ne saboda boye laifukan yakin da HKI take aikatawa a Gaza da kuma sauran yankunan Falasdinawa da take mamaye da su.
A wani jawabin da ta gabatar a gaban kwamitin tsaro na MDD a ranar Laraba mai rike da mukamin jakadan Amurka a MDD Dorothy Shea ta bayyanawa kwamitin tsaro kan cewa dole kungiyar Hamas ta mika makamanta sannan da ita da sauran Falasdinawa su bar Gaza su je inda suka ga dama.
Bayan jawabinta ne Iravani ya rbutawa babban sakataren MDD da kuma shugaban kwamitin tsaro na wannan wato Carolyn Rodrigues-Birkett wasika inda yake musanta zarge zargen na Amurka.