Gaza : Sabon kisan kiyashi a kusa da wurin rarraba kayan abinci
Published: 2nd, June 2025 GMT
Jami’ai a Falasdinu sun ce akalla mutum 31 ne sukayi shahada sannan wasu sama da 150 sun jikkata, bayan wani hari da Isra’ila ta kai kusa da wurin rabon abinci a birnin Rafah.
Dama shugaban hukumar MDD da ke kula da yan gudun hijirar Falasdinawa, Philippe Lazzarini, ya ce rabon kayan agajin ya zama tarkon mutuwa.
Lamarin dai ya faru ne a kusa da wata cibiyar rarraba kayan abinci da gidauniyar agaji ta Gaza (GHF) ke gudanarwa, wani kamfani mai zaman kansa da ke samun goyon bayan Isra’ila da Amurka da kungiyoyin agaji na kasa da kasa suka yi suka.
Kakakin kungiyar Hamas Sami Abu Zohri yayi Allah wadai da gwamnatin Isra’ila kan harin da ta aikata a rabon kayan agaji a Gaza, Inda ya jaddada cewa an yi wannan kisan kiyashi ne tare da goyon bayan Amurka.
Dangane da wannan kisan kiyashi da zubar da jinin shahidai, ya yi kira ga dukkanin al’ummar musulmi da masu son ‘yanci a fadin duniya da su tashi tsaye wajen yakar masu kisan gillar da sahyoniyawa ke yi.
A wani share kuma kungiyar gwagwarmayar Falasdinawan ta yi kira ga Majalisar Dinkin Duniya, da cibiyoyinta, musamman ma kwamitinta na tsaro, da su dauki matakan da suka dace don tilastawa gwamnatin Isra’ila ta kawo karshen zubar da jini da take yi, tare da gaggauta bude mashigar Zirin da aka yi wa kawanya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
Majiyar ta kara da cewa, bayan yunkurinsu bai yi nasara ba a Tsanyawa, maharan sun sake wani sabon shiri, inda suka kai hari a kauyen Yar Tsamiya da ke gundumar Faruruwa, karamar hukumar Shanono, da misalin karfe 1:30 na dare, inda suka kashe mutane uku suka, tare da sace wasu uku.
Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA