Gaza : Sabon kisan kiyashi a kusa da wurin rarraba kayan abinci
Published: 2nd, June 2025 GMT
Jami’ai a Falasdinu sun ce akalla mutum 31 ne sukayi shahada sannan wasu sama da 150 sun jikkata, bayan wani hari da Isra’ila ta kai kusa da wurin rabon abinci a birnin Rafah.
Dama shugaban hukumar MDD da ke kula da yan gudun hijirar Falasdinawa, Philippe Lazzarini, ya ce rabon kayan agajin ya zama tarkon mutuwa.
Lamarin dai ya faru ne a kusa da wata cibiyar rarraba kayan abinci da gidauniyar agaji ta Gaza (GHF) ke gudanarwa, wani kamfani mai zaman kansa da ke samun goyon bayan Isra’ila da Amurka da kungiyoyin agaji na kasa da kasa suka yi suka.
Kakakin kungiyar Hamas Sami Abu Zohri yayi Allah wadai da gwamnatin Isra’ila kan harin da ta aikata a rabon kayan agaji a Gaza, Inda ya jaddada cewa an yi wannan kisan kiyashi ne tare da goyon bayan Amurka.
Dangane da wannan kisan kiyashi da zubar da jinin shahidai, ya yi kira ga dukkanin al’ummar musulmi da masu son ‘yanci a fadin duniya da su tashi tsaye wajen yakar masu kisan gillar da sahyoniyawa ke yi.
A wani share kuma kungiyar gwagwarmayar Falasdinawan ta yi kira ga Majalisar Dinkin Duniya, da cibiyoyinta, musamman ma kwamitinta na tsaro, da su dauki matakan da suka dace don tilastawa gwamnatin Isra’ila ta kawo karshen zubar da jini da take yi, tare da gaggauta bude mashigar Zirin da aka yi wa kawanya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
MDD : Gaza na cikin bala’i mafi muni tun soma yaki a Zirin a Oktoban 2023
Wani rahoto da ofishin kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya ya fitar, ya nuna cewa Gaza na fuskantar bala’i mafi muni tun soma yaki a Zirin a watan Oktoban 2023.
Wakilin Majalisar Dinkin Duniya na musamman kan hakkin bil adama a yankunan Falasdinawa da aka mamaye ya zargi gwamnatin Isra’ila da yin amfani da batun agajin jin kai da gangan domin ci gaba da aiwatar da munanan laifukan da take aikatawa a Gaza.
Francesca Albanese a cikin wata sanarwa da ta fitar ta ce: “Dukkan wadannan matakan an boye su ne a karkashin sunan agaji don karkatar da hankulan kasashen duniya.”
A wani labarin kuma Kakakin Majalisar Dinkin Duniya Stéphane Dujarric ya shaida wa manema labarai a ranar Juma’a da ta gabata cewa: Bukatun jin kai a Gaza ya karu sosai bayan kusan kwanaki 80 na hana shigar da tallafi a zirin.
‘’tallafin da ake samu a yanzu haka bai wadatar ba wajen biyan bukatun mutane sama da miliyan 2.1 da ke bukatar agajin gaggawa. » inji shi.
Adadin wadanda sukayi shahada a wannan yanki na Falasdinu tun daga ranar 7 ga watan Oktoban shekarar 2023 ya kai mutane 54,381, a cewar ma’aikatar lafiya ta Gaza.