Fransa Ta Kira Yi Kasashen Turai Da Sake Bitar Alakarsu Da “Isra’ila”
Published: 20th, May 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Faransa ya kira yi tarayyar turai da ta sake bitar alakarta da Isra’ila saboda ci gaba da kisan kiyashin da take yi wa al’ummar Gaza da kuma hana shigar da kayan agaji.
Matakin na Faransa dai ya biyo bayan na kasashen Spain, Ireland da kuma Holland, da suke son ganin an gudanar da bincike akan ko hare-haren Gaza din sun karya wani sashe na yarjejeniyar tasu.
Tun a cikin watan Yuni na 2000 ne nahiyar turai din ta kulla yarjejeniyar ayyuka a tsakaninta da HKI a fagage da dama, da hakan ya bai wa Tel Aviv fifiko na musamman a cikin kasuwannin turai. Harkokin kasuwanci a tsakaninsu ya kai dala biliyan 46.8 a 2022.
Ministan harkokin wajen Faransa Jean-Noël Barrot ya bayyana cewa; Saboda matsayar Isra’ila akan gaza, ya zama wajibi a yi bitar alakarta da tarayyar turai.
Barrot ya bayyana tsananta hare-haren akan Gaza da kuma hana shigar da kayan abinci da cewa ” Ba abu ne da za a lamunta da shi ba.”
Haka nan kuma ya bayyana hare-haren na Isra’ila da cewa; cin zarafin Karaman dan’adam ne da kuma keta dokokin kasa da kasa, kuma yana cin karo da tsaron Isra’ila da Faransa ta yi alkawalin karewa,to amma duk abinda mutum ya shuka shi zai girba.
Gabanin Faransa, Faransa, kasar Holland ta yi kira irin wannan na yin bitar alaka da Isra’ila,wacce ministan harkokin wajen na Faransa ya ce, yana goyon baya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Aragchi: Iran Ba zata Taba Daina Tace Makamashin Uranium A Cikin Gida Ba
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa shirin makamashin nukliya na kasar Iran kuma na zaman lafiya ya zama abin alfakhari ga mutanen kasar da daukaka. Don haka gwamnati mutanen kasar ba zasu taba yarda a barshi ba.
Ministan ya bayyana haka ne a lokacin da yake hira da tashar talabijin ta CBS news na kasar Amurka dangane da hare-haren da HKI da kuma Amurka suka kaiwa kasar a cikin watan yuni da ya gabata. Hare-haren da aka kaiwa kasar a dai-dai lokacinda take tattaunawa da Amurka.
A wani bangare a maganars Aragchi ya bayyana cewa baya ganin Iran zata farfado da tattaunawa da kasar Amurka nan kusa.
Ya ce: Idan har zamu sake shiga tattaunawa da Amurka sai mun tabbatar da cewa Amurka ba zata kuma kai mana hare-hare a dai-dai lokacinda muke tattaunawa ba.
Ya kara da cewa, tare da wannan tunanin muna ganin sake zama da Amurka kan teburin tattauna ba nan kusa ba. Daga karshe ya ce: a duk sanda muka ga dama ta samu, bama rufe kofar tattaunawa da kowa .
Da aka tamabaye shi dangane da shirin makamashin Nukliya na kasar bayan bom da aka jefa masu. Ministan ya ce: Ai ba’a kauda shirin nukliya da bom. Ko babu shi kwata-kwata zamu sake gina wani daga farko. Sannan idan sun baci ne muna iya sake gyaransu sai mu ci gaba.