Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Mele Kyari

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya bayar umarnin binciken hare-haren Benuwe

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya umarci jami’an tsaro da su yi bincike tare da gano waɗanda suka kai hari a Jihar Benuwe, inda aka kashe sama da mutum 100.

Harin ya faru ne a ƙauyen Yelwata da ke Ƙaramar Hukumar Guma a jihar.

Iran ta rataye mutumin da ta kama yana yi wa Isra’ila leƙen asiri KADSEMA da IOM sun fara tantance ɓarnar da ambaliya ta yi a Kaduna

Bayan harin, matasa sun rufe hanyar Lafiya zuwa. Makurdi domin nuna ɓacin ransu.

Zanga-zangar ta ci gaba da gudana har zuwa safiyar ranar Lahadi a birnin Makurdi, babban birnin jihar.

Rundunar ‘yan sandan jihar ta yi amfani da barkonon tsohuwa domin tarwatsa masu zanga-zangar.

A daren ranar Lahadi, Shugaba Tinubu ya wallafa saƙo a a shafin sa na X, inda ya ce dole a kawo ƙarshen wannan kashe-kashe, kuma ya umarci jami’an tsaro su ɗauki mataki don kama duk masu hannu a rikicin.

Tinubu ya kuma buƙaci Gwamnan Jihar Benuwe, Hyacinth Alia, da ya jagoranci tattaunawa da yin sulhu tsakanin manoma da makiyaya domin wanzar da zaman lafiya.

Ya gargaɗi shugabannin siyasa da na al’umma da su guji furucin da ka iya haifar da tarzoma.

Ya ce lokaci ya yi da za a haɗa kai domin warware matsaloli da hanyar gaskiya, adalci da fahimta, domin a samu zaman lafiya a Jihar Benuwe.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya
  • Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu
  • Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53
  • Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran
  • Tinubu ya bayar da umarnin binciken hare-haren Benuwe
  • Tinubu ya bayar umarnin binciken hare-haren Benuwe
  • KADSEMA da IOM sun fara tantance ɓarnar da ambaliya ta yi a Kaduna
  • Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas
  • Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya
  • Cece-Kuce Ya Barke Bayan Ganduje Da Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas Sun Nemi A Sauya Shettima A 2027