“Manchester United ce fa kowane dan wasa na hankoron taka wasa a cikinta kuma idan kuka duba kungiyar a yanzu, kamar akwai matsaloli, ciki har da sauya koci da aka yi amma duk da haka muna da masaniyar abin da ya kamata, kuma abu ne mai sauki a ganar da dan wasa” in ji Amorim, wanda ya koma United daga Sporting Lisbon.

 

Ya kara da cewa magana ce ta karshen kaka kuma komai zai iya sauyawa. Amma dai suna so su fara komai da wuri kuma sun san yadda za su yi hakan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Fatattaki Laifukan Zamba Ta Shafin Intanet 294,000 A Bara

A wani gangamin magance aikata laifukan zamba da damfara ta shafukan intanet da kasar Sin ta kaddamar a fadin kasar baki daya, ‘yan sandan kasar ta Sin sun fatattaki laifuka 294,000 a shekarar 2024, inda suka kama mutane da dama da ake zargi ciki har da shugabanni gungu-gungu fiye da 570, da masu samar musu da kudi, da kuma kasurguman da ke da hannu a wannan ta’asar.

‘Yan sanda sun durfafi cibiyoyin sadarwa na masu aikata laifuka da ke ba da haramtaccen tallafi ga aikata ayyukan zamba a kasashen ketare. A cewar ma’aikatar kula da tsaron al’umma, wadannan kungiyoyin sun tafka ta’asa masu yawa da suka hada da tallata laifukan a shafin intanet, da satar kudi, da amfani da fasaha, da kuma taimakawa wajen saukake hanyoyin tsallaka kan iyakokin kasa.

Tun daga farkon shekarar 2024, cibiyar yaki da zamba ta kasar Sin ta kara kaimi wajen yin gargadi a kan lokaci da kuma daukar matakan dakile ta’asar ta hanyar amfani da fasahohin zamani, inda ta ba da sanarwa game da hakan sau miliyan 1.8. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo
  • Litar fetur za ta iya komawa N1,000 a Najeriya saboda yakin Isra’ila-Iran – Masana
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kwaso ‘Yan Nijeriya Da Suka Maƙale A Isra’ila Da Iran
  • Ambaliyar Mokwa – Har yanzu muna neman mutum 700 – Gwamnatin Neja
  • 2025 UTME: Cibiyoyin Zana Jarabawar 11 Na Fuskantar Barazanar Dakatarwa – JAMB
  • Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas
  • Sin Ta Fatattaki Laifukan Zamba Ta Shafin Intanet 294,000 A Bara
  • Atalanta Na Neman Yuro Miliyan 50 Daga Duk Kungiyar Da Ke Son Daukar Lookman
  • IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 
  • Iran ta kai sabbin hare-hare birnin Tel Aviv da Haifa