HausaTv:
2025-05-22@01:18:06 GMT

WHO, ta nuna kaduwa da abin da ke faruwa a Gaza

Published: 1st, May 2025 GMT

Hukumar lafiya ta Duniya WHO, ta nuna matukar kaduwa game da halin da ake ciki a Gaza.

Abin da ke faruwa a Gaza “ba abinda za’a lamunta da shi ne ba,” in ji Mike Ryan, mataimakin darekta-janar na Hukumar Lafiya ta Duniya, yayin wani taron manema labarai.

Mista Ryan, ya nuna fushinsa matuka game da rashin tabaka komai na taimaka wa jama’a a zirin Gaza.

“Muna wargaza tunani da jikin yaran Gaza, ga yunwa ga yaran Gaza, idan ba mu dauki mataki ba, za mu shiga cikin abin da ke faruwa a idanunmu,” in ji shi.

A gobe Juma’a ne za a cika watanni biyu na hana shigar da kayan agaji da sojojin Isra’ila suka yi a zirin Gaza baki daya.

Tun a ranar 2 ga Maris, ba a ba da izinin shigar da kayan agajin jin kai ba, a matakin da Isra’ila ta ce na tilasta wa kungiyar Hamas ne sakin mutanen da aka yi garkuwa da su a harin ba zata na ranar 7 ga watan Oktoba 2023.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano ta dakatar da haska shirin Labarina da Dadin Kowa da wasu 20

Hukumar tace fina-finai ta Jihar Kano ta dakatar da haska shirin Labarina, Dadin Kowa da wasu ƙarin fina-finan Hausa guda 20 a kafafen Internet ko gidajen talabijin.

Hukumar ta ce ta ɗauki matakin ne a ƙoƙarinta na tabbatar da ana bin dokar tace fina-finai sau da ƙafa tare da ƙara dora masana’antar Kannywood a kan saiti.

A cewar wata sanarwar da jami’in yaɗa labarai na hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman, ya fitar da daren Lahadi, fina-finan da dakatarwar ta shafa sun haɗa da Labarina, Dadin Kowa, Manyan Mata, Garwashi, Jamilun Jidda da kuma Gidan Sarauta.

Sanarwar ta ce umarnin ya fito ne daga bakin shugaban hukumar, Abba El-Mustapha, bayan wani zamanta da kuma tattaunawar da ta gudanar.

An kama ƙasurgumin ɗan bindiga yayin tantance alhazai a Abuja Jami’in Sibil Difens ya mayar da N800,000 da wata Hajiya ta zubar a Adamawa Jerin fina-finan da aka dakatar

Sanarwar ta bayyana jerin fina-finan da dakatarwar kamar haka:

Ɗakin Amarya Mashahuri Wasiyya Tawakkaltu Mijina Wani Zamani Mallaka Kuɗin Ruwa Boka Ko Malam Wa Ya San Gobe Rana Dubu Manyan Mata Fatake Gwarwashi Jamilun Jiddan Shahadar Nabila Daɗin Kowa Tabarma Kishiyata da kuma Rigar Aro.

Hukumar ta ce ta ɗauki gagarumin matakin ne domin tsaftace yadda ake sakin fina-finai barkatai ba tare da cika ƙa’idar da doka ta tanadar musu ba na kawo kowanne fim gabanta a tantance shi kafin a sake shi.

Sanarwar ta kuma ce doka ce ta ba Hukumar damar tace duk wani fim tare da lura da ayyukan ’yan masana’antar Kannywood matukar suna da rajista da hukumar a ko ina suke.

“A saboda haka, ana shawartar masu ɗaukar nauyin waɗannan fina-finai da su tabbatar da sun bi wannan doka ta dakatarwa tare da tsayar da saka wannan fina-finai a gidajen talabijin ko kafar internet.

“Haka kuma ana sanar da su cewa su miko fina-finansu ga hukumar domin tantance su tare da ba su shaidar inganci ta tacewa nan da sati ɗaya mai zuwa wato daga Litinin, 19 ga watan Mayu, 2025 zuwa 25 ga Mayu, 2025 domin gujewa fushin doka,” in ji sanarwar.

Tun bayan canjin da kasuwar fina-finai dai ta samu da ya sa kuɗaɗen da ake samu a sayar da fina-finai suka yi ƙasa sosai, galibin ’yan masana’antar Kannywood suka koma shirya fina-finai masu dogon zango domin a ci gaba da damawa da su.

Akan ɗora fina-finan ne a dandalin YouTube da wasu gidajen talabijin a mako-mako.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar tace fina-finai ta soke lasisin gidajen gala 8 a Kano
  • Mun dakatar da sanya tallan magungunan gargajiya a fina-finai – Abba
  • Shugaban Kasar Colombia: Ayyukan Kasar Sin Sun Nuna Wani Sabon Salo Na Ci Gaban Zamantakewar Al’ummar Bil’adama
  • Kasashen duniya 22 sun bukaci Isra’ila da ta dawo da agaji gaba daya a Gaza
  • HKI Ta Bude Kofofin Shigar Kayakin Agaji Zuwa Cikin Gaza A Karon Farko Bayan Kimani Watanni 2.5
  • Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Nuna Wasu Manyan Fina-Finai 22
  • Wata ‘Yar Jarida Ta Nuna Mamaki Kan Nuna Damuwa Da Ciwon Biden Maimakon Kisan Gillar ‘Yan Sahayoniyya
  • NAJERIYA A YAU: Mece ce Makomar Dimokuraɗiyya Idan Aka Wajabta Kada Kuri’a?
  • Falasdinu : ‘Yan jarida 222 aka kashe tun fara yakin Gaza
  • Gwamnatin Kano ta dakatar da haska shirin Labarina da Dadin Kowa da wasu 20