Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-08-01@09:13:25 GMT

Inter Milan Ta Je Ta Rike Barcelona A Champions League

Published: 1st, May 2025 GMT

Inter Milan Ta Je Ta Rike Barcelona A Champions League

An tashi 3-3 tsakanin Barcelona da Inter Milan a wasan farko zagayen daf da karshe a Champions League da suka kara a Sifaniya ranar Laraba.

Inter Milan ce ta fara cin ƙwallo a daƙiƙa 30 da take leda ta hannun Marcus Thuram, ya zama na farko da ya ci ƙwallo a ƙanƙanin lokaci a daf da karshe a Champions League.

Daga nan Inter ta kara na biyu ta hannun Denzel Dumfries, wanda ya zama na farko daga Netherlands da ya ci ƙwallo ya kuma bayar aka zura a raga a daf da karshe a Champions League, tun bayan Wesley Sneijder a Inter a karawa da Barcelona.

Dumfries shi ne ya bai wa Thuram ƙwallon farko da Inter Milan ta zura a ragar Barcelona cikin ƙanƙanin lokaci.

Barcelona ta sa namijin ƙwazo a wasan, inda Lamine Yamal ya zare ɗaye a minti na 24 a wasan na hamayya.

Haka kuma ƙungiyar Sifaniya ta farke na biyun ta hannun Ferran Torres, bayan da Raphinha ya samar masa damar zura ƙwallon a cikin raga cikin sauƙi.

Ana tsaka da wasa Inter Milan ta kara na uku ta hannun Denzel Dumfries, sai dai minti biyu tsakani mai tsaron ragar Inter, Yann Sommer ya ci gida.

Kenan ta sanadin Raphinha, wanda shi ne ya buga tamaular – hakan ya sa ya yi kan-kan-kan da Cristiano Ronaldo, wanda yake da hannu a cin ƙwallo 20 a Champions League a 2013/14.

Raphinha, ɗan wasan tawagar Brazil, ya zura 12 a raga ya kuma yi sanadin cin tara a bana a babbar gasar tamaula ta nahiyar Turai.

Barcelona da Inter Milan sun fuskanci juna karo na 17 a babbar gasar zakarun Turai, inda ƙungiyar Sifaniya ta yi nasara takwas da canjaras shida aka doke ta wasa uku.

Barcelona ta yi wasa shida ba tare da an doke ta ba a gida a fafatawa da Inter Milan kenan a Champions League, wadda ta yi nasara biyar da canjaras ta biyu.

Kocin Inter Milan, Simone Inzaghi, ya ja ragamar wasa na 50 a Champions League, ya zama mai horarwa na bakwai daga Italiya da ya yi wannan ƙwazon.

Ranar Talata 6 ga watan Mayu, Inter Milan za ta karɓi bakuncin Barcelona a wasa na biyu zagayen daf da karshe a Champions League a Italiya.

Barcelona ta kawo wannan matakin bayan yin waje da Borussia Dortmund, ita kuwa Inter Milan ita ce ta fitar da Bayern Munich a zagayen kwata fainal.

Barcelona tana matakin farko a teburin La Liga da tazarar maki huɗu tsakani da Real Madrid ta biyu a kakar nan.

Ita kuwa Inter Milan tana ta biyun teburin Serie A da tazarar maki uku tsakani da Napoli mai jan ragamar babbar gasar tamaula ta Italiya.

Inter za ta karɓi bakuncin Verona a gasar Serie A ranar Asabar 3 ga watan Mayu, sannan ta kece raini da Barcelona a Italiya a Champions League ranar Talata.

Barcelona kuwa za ta je gidan Valladolid a gasar La Liga ranar Asabar 3 ga watan Mayu, sannan ranar Talata ta ziyarci Inter a wasa na biyu a Champions League.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Wasani daf da karshe a Champions League Barcelona ta

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu

Gwamna Zulum ya nuna jin dadinsa ga kwamishinonin biyu, tare da yi musu fatan alheri a cikin ayyukansu na gaba.

 

Sai dai ya sanar da nadin Engr. Mohammed Habib da Ibrahim Hala Hassan domin maye gurbin kwamishinonin biyu da aka sauke.

 

A halin da ake ciki, Gwamna Zulum ya kuma amince da nadin Farfesa Yusuf Gana Balami a matsayin Shugaban Hukumar Ilimin Sakandare ta Jihar Borno.

 

Balami, Farfesa a fannin ilimi, ya fito ne daga Hawul da ke kudancin jihar.

 

Zulum ya taya Balami murna tare da bukatar sa da ya yi amfani da shekarunsa na gogewa a fannin ilimi, a matsayin shugaba a bangaren gudanarwa da karantarwa wajen sake fasalin ilimin sakandare a jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu
  • Kananan Yan Wasan Dabben Gargajiya Na Iran Sun Zama Zakara A Gasar Wannan Shekara
  • Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta
  • Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza
  • Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
  • Rashin Nasarar DPP A Zagayen Farko Na Kuri’ar Kiranye Ya Nuna Rashin Amincewar Al’ummar Taiwan Da Salon Mulkin Jami’yyar
  • Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu
  • Shugaban Ivory Coast Ouattara zai sake takara wa’adi na huɗu
  • Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON