Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-06-15@22:20:47 GMT

Inter Milan Ta Je Ta Rike Barcelona A Champions League

Published: 1st, May 2025 GMT

Inter Milan Ta Je Ta Rike Barcelona A Champions League

An tashi 3-3 tsakanin Barcelona da Inter Milan a wasan farko zagayen daf da karshe a Champions League da suka kara a Sifaniya ranar Laraba.

Inter Milan ce ta fara cin ƙwallo a daƙiƙa 30 da take leda ta hannun Marcus Thuram, ya zama na farko da ya ci ƙwallo a ƙanƙanin lokaci a daf da karshe a Champions League.

Daga nan Inter ta kara na biyu ta hannun Denzel Dumfries, wanda ya zama na farko daga Netherlands da ya ci ƙwallo ya kuma bayar aka zura a raga a daf da karshe a Champions League, tun bayan Wesley Sneijder a Inter a karawa da Barcelona.

Dumfries shi ne ya bai wa Thuram ƙwallon farko da Inter Milan ta zura a ragar Barcelona cikin ƙanƙanin lokaci.

Barcelona ta sa namijin ƙwazo a wasan, inda Lamine Yamal ya zare ɗaye a minti na 24 a wasan na hamayya.

Haka kuma ƙungiyar Sifaniya ta farke na biyun ta hannun Ferran Torres, bayan da Raphinha ya samar masa damar zura ƙwallon a cikin raga cikin sauƙi.

Ana tsaka da wasa Inter Milan ta kara na uku ta hannun Denzel Dumfries, sai dai minti biyu tsakani mai tsaron ragar Inter, Yann Sommer ya ci gida.

Kenan ta sanadin Raphinha, wanda shi ne ya buga tamaular – hakan ya sa ya yi kan-kan-kan da Cristiano Ronaldo, wanda yake da hannu a cin ƙwallo 20 a Champions League a 2013/14.

Raphinha, ɗan wasan tawagar Brazil, ya zura 12 a raga ya kuma yi sanadin cin tara a bana a babbar gasar tamaula ta nahiyar Turai.

Barcelona da Inter Milan sun fuskanci juna karo na 17 a babbar gasar zakarun Turai, inda ƙungiyar Sifaniya ta yi nasara takwas da canjaras shida aka doke ta wasa uku.

Barcelona ta yi wasa shida ba tare da an doke ta ba a gida a fafatawa da Inter Milan kenan a Champions League, wadda ta yi nasara biyar da canjaras ta biyu.

Kocin Inter Milan, Simone Inzaghi, ya ja ragamar wasa na 50 a Champions League, ya zama mai horarwa na bakwai daga Italiya da ya yi wannan ƙwazon.

Ranar Talata 6 ga watan Mayu, Inter Milan za ta karɓi bakuncin Barcelona a wasa na biyu zagayen daf da karshe a Champions League a Italiya.

Barcelona ta kawo wannan matakin bayan yin waje da Borussia Dortmund, ita kuwa Inter Milan ita ce ta fitar da Bayern Munich a zagayen kwata fainal.

Barcelona tana matakin farko a teburin La Liga da tazarar maki huɗu tsakani da Real Madrid ta biyu a kakar nan.

Ita kuwa Inter Milan tana ta biyun teburin Serie A da tazarar maki uku tsakani da Napoli mai jan ragamar babbar gasar tamaula ta Italiya.

Inter za ta karɓi bakuncin Verona a gasar Serie A ranar Asabar 3 ga watan Mayu, sannan ta kece raini da Barcelona a Italiya a Champions League ranar Talata.

Barcelona kuwa za ta je gidan Valladolid a gasar La Liga ranar Asabar 3 ga watan Mayu, sannan ranar Talata ta ziyarci Inter a wasa na biyu a Champions League.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Wasani daf da karshe a Champions League Barcelona ta

এছাড়াও পড়ুন:

Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Kakkabo Jiragen Yakin Isra’ila Biyu Kirar F-35

Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta zama kasa ta farko a duniya da ta harbo jiragen saman yaki kirar F-35

Iran ta zama kasa ta farko a duniya da ta yi nasarar harbo jiragen yaki kirar F-35, bayan da ta yi nasarar auna wasu jiragen saman yakin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila kirar F-35 guda biyu, kuma ta barar da su kasa.

Gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta yi amfani da wadannan jirage masu tsananin ci gaban zamani wajen kai hare-haren wuce gona gona da iri kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran da safiyar ranar Juma’a, wanda hare-haren suka yi sanadiyyar shahadar wasu manyan jami’an sojan Iran da masana kimiyyar nukiliya da fararen hula da suka hada da mata da kananan yara.

Ma’aikatar hulda da jama’a ta rundunar sojojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta sanar a cikin wata sanarwa da ta fitar cewa: Dakarun tsaron saman Iran sun harbo jiragen saman yaki kirar F-35 guda biyu, baya ga wasu jiragen saman yakin yahudawan sahayoniyya marasa matuka ciki.

Sanarwar ta nuna cewa: Jami’an tsaron Iran sun kame daya daga cikin matukan jiragen wacce mace ce, kuma ana kan bincike domin sanin makomar matukin daya jirgin.

Abin lura shi ne cewa: Jiragen yakin kirar F-35 da ‘yan sahayoniyya ke amfani da su na daga cikin wadanda suka ci gaba a duniya kuma ake gwada su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Cilla Makamai Kan HKI Da Rana A Karon Farko A Yau Lahadi
  • APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu
  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • Martanin Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Kan Ta’addancin ‘Yan Sahayoniyya ya Shiga Rana Ta Biyu
  • ‘Yan Wasa Biyar Da Suka Taka Rawar Gani A Kofin Zakarun Turai
  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila
  • Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Kakkabo Jiragen Yakin Isra’ila Biyu Kirar F-35
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya