Yobe na ɗaya daga cikin jihohin Najeriya mafi zaman lafiya – Buni
Published: 24th, April 2025 GMT
Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya ce a yanzu jihar na ɗaya daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya a Najeriya.
Ya ce, a matsayinsa na babban jami’in shari’a da tsaro a Jihar Yobe, yana da haƙƙin ganin an bi doka don tabbatar da cewa jihar ta samu zaman lafiya.
An kama mata 2 na ƙoƙarin sayar da ƙananan yara da aka sace An fara raba wa almajirai tabarma da gidan sauro a YobeGwamnan ya bayyana hakan ne a yayin karɓar lambar karramawa da aka yi masa shi da wasu shugabnnin da Ƙungiyar Inganta zaman lafiya ta “Peace Building Development Consult” (PBDC) ta yi musu.
Gwamnan wanda ya samu wakilcin babban lauya kuma Kwamishinan Shari’a na Jihar Yobe, Barista Saleh Samanja, ya bayyana hakan ne ga manema labarai ranar Laraba a Abuja, bayan da ya karɓi lambar yabon ta zaman lafiya.
“ina tabbatar muku kai tsaye cewar, Jihar Yobe tana ɗaya daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya a Najeriya, hakan yana yiwuwa ne saboda haɗin kan da muke bai wa jami’an tsaro da kuma namijin ƙoƙarin da Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni ke yi na bada gudummawa kan harkokin tsaro da duk abin da hukumomin tsaro ke son gwamnati ta yi.
“A matsayinsa na babban jami’in shari’a da tsaro na jihar, yana jin cewa yana da haƙƙin ɗabi’a da na shari’a don ba da haɗin kai ga hukumomin tsaro domin mu samu cikakken zaman lafiya a Jihar Yobe,” in ji shi.
A cewarsa wannan karramawar na ƙara ƙarfafa gwiwa ne, inda ya ce Gwamnan zai ci gaba da yin abin da yake yi domin ganin an dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: zaman lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
Tsohon Gwamnan Jihar Ekiti, Kayode Fayemi, ya ce har yanzu Najeriya ba ta kai matsayin cin ribar cikakkiyar dimokuraɗiyya ba, duk da cewa an dawo mulkin farar hula shekaru 26 da suka gabata.
Yayin wata tattaunawarsa da gidan talabijin na Channels, domin bikin Ranar Dimokuraɗiyya, Fayemi ya bayyana cewa duk da cewa ana gudanar da zaɓe a kai a kai a ƙasar, har yanzu an rasa muhimman abubuwan da suka kamata su kasance a tsarin dimokuraɗiyya na gaskiya.
Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna“Bai kamata mu rikita gudanar da zaɓe da aiwatar da dimokuraɗiyya ba,” in ji shi.
“Abin da muka samu a 1999 shi ne ’yancin zaɓar shugabanni, amma hakan kawai ɓangare ne guda ɗaya.
“Abin da muke da shi mulkin farar hula ne, ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba.”
Ya ce an samu ci gaba a ƙarƙashin gwamnatoci daban-daban tun daga baya, amma har yanzu Najeriya na buƙatar ƙarfafa al’adar dimokuraɗiyya da sauye-sauyen da suka dace.
Fayemi ya kuma tuna da lokacin da ya kasance ɗaya daga cikin masu fafutukar dimokuraɗiyya a zamanin mulkin soja, musamman a lokacin marigayi Janar Sani Abacha.
Ya bayyana yadda suka gudanar da shirye-shirye a wani gidan rediyo a aka ɓoye, don ƙalubalantar gwamnatin soji.
“Ba wai rashin tsoro ba ne, mun san hatsarin da ke tattare da lamarin, amma mun yi imani da abin da muke yi,” in ji shi.
“Na taɓa ɗaukar na’urar watsa shirye-shiryen rediyon Kudirat a cikin jirgin Air France da ya sauka a Legas lokacin da fafutukar ta yi zafi. Wannan kaɗai na iya jefa ni cikin hatsari.”
Ya ce waɗanda suka mutu a lokacin ba don sakaci suka rasa rayukansu ba, sai don sun gaskata ƙudurinsu na ganin an samu ’yanci.
Fayemi ya yaba wa Shugaba Bola Tinubu bisa karrama wasu daga cikin waɗanda suka fafata wajen dawo da dimokuraɗiyya.
Sai dai ya nuna damuwa cewa wasu da dama da suka taka muhimmiyar rawa a bayan fage ba a karrama su ba.
“Mutane da dama sun sa rayuwarsu cikin hatsari. Su ma sun cancanci a yaba musu.
“Ba daidai ba ne a girmama waɗanda ake gani a manta da waɗanda suka bayar da gudunmawarsu a bayan fage.”
Maganganun Fayemi sun haifar da zazzafar muhawara kan yadda Najeriya ke da buƙatar ci gaba kafin a kira ta da ƙasar da ke da cikakkiyar dimokuraɗiyya.