HausaTv:
2025-09-17@23:28:47 GMT

Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 112

Published: 23rd, April 2025 GMT

112-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissiso da suka zo cikin alkur’ani mai girma ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin dastane rastan, ko kum littafin mathnawi na maulana Jalaluddeen rumi.

Ko kuma cikin wasu littafan da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu a cikin shirimmu na yau.

///… Masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, a kuma cikin sirar Imam Al-hassan limami na biyu daga cikin limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All..(s), kuma da na farko ga Fatimah diyar manzon All..(s), sannan jikansa na farko.

A cikin shirimmu da ya gabata mun kawo maku yadda Abuzar a Alghifari babban sahabin manzon All..(s) wanda ya kasance daga cikin mutane na farko da suka musulunta a Makka, sannan ya kuma garinsu giffar yana kiran mutane zuwa ga addinin musulunci har zuwa lokacinda manzon All..(s) yayi hijira, zuwa Madina sai shi ma yayi hijira. Banda haka, manzon All..(s) ya yabeshi a cikin hadisai da dama saboda tsoron All..ta zuhudu da kuma sanin addini.

Amma a lokacinda Uthman bin Affan ya  zama khalifa ya kuma dora danginsa Banu Umayya a kan al-ummar musulmi suna azabtar da shi suna kuma kwasar kudaden jama’a suna kashewa kansu, ya fuskanci matsaloli da sahabban manzon All..(s) da dama daga ciki har da Abuzar Alghiffari, wanda ya ci gaba da sukar khalifa da kuma danginsa, har sai da ya kore shi daga madina zuwa Sham da farko, sannan ya sake dawo da shi Madina a cikin mummunan hali, amma Abuzar bai dandara ba, ya ci gaba da sukansu har sai da wata rana, Khalifa yayi tambaya a kan al-amuran addini sai wani bayahude wanda bai dade da musulunct ba, ya bada amsa kuma ba dai dai ba, sai Abuzar ya tashi a kasansa, sai Khalifa kuma ya tashi a kan Abuzar yana masa tsawa, daga karshe ya sake korarsa daga Madina karo na biyu, amma a wannan karon ya kore shi zuwa wani daji inda babu mutane, kuma yace zai zauna a wurin har sai ya mutunu.

Munji yadda ya umurci Marwan dan hakam, ya bashi guzuri ya koma can inda ba zai ga wani ba, kuma ba wanda zai ganshi. Sai Marwan ya ajiye shi a wani wuri kafin ya kammala hada masa guzuri, sannan khalifa ya fadawa Marwan ya fitar da shi cikin kaskanci daga Madina sannan kada ya bar kuma ya yi magana da shi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato

Gwamnan Sakkwato, Dakta Ahmad Aliyu, ya ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani guda 20, tare da riguna ruwa (life jackets) 2,000, domin rage haɗurran da ke aukuwa sakamakon ambaliya da nutsewar jirage a sassan jihar.

An ƙaddamar da jiragen ne a ƙaramar hukumar Wamakko a ranar Laraba, inda gwamnan ya bayyana cewa wannan mataki na daga cikin shirin gaggawa na tallafa wa al’ummar da ke fama da illar ambaliya da haɗurra a ruwa.

Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB

“Mun dauki wannan mataki bayan rahotannin da muke samu na yawaitar hatsarurruka da rasa rayuka da dukiya sakamakon jiragen katako da mutane ke amfani da su,” in ji Gwamna Ahmad Aliyu.

Gwamnan ya miƙa godiya ga shugabar hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA), Hajiya Zubaida Umar, bisa hadin kai da goyon bayan da hukumar ke bayarwa domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiya, tare da inganta ayyukan ceto da agaji a jihar.

Aminiya ta ruwaito cewa, an horar da direbobin jiragen ruwan da za su riƙa kula da su, kafin a raba su zuwa ƙananan hukumomi goma (10) da suka fi fuskantar barazanar ambaliya da suka haɗa da: Goronyo, Shagari, Sabon-Birni, Wurno, Rabah, Wamakko, Silame, Kebbe, Tambuwal da Isa.

Gwamnan ya kuma yi gargaɗin cewa za a hukunta duk wani da ya ɗauki lodi fiye da ƙima a cikin jiragen, yana mai cewa “wannan jirage da rigar ruwa na jama’a ne, kuma wajibi ne shugabannin ƙananan hukumomi su tabbatar da kula da su yadda ya kamata.”

Sai dai wasu daga cikin mazauna yankunan da za a rabawa jiragen sun bayyana ra’ayinsu dangane da lamarin, inda wani Tanimu Goronyo, daga karamar hukumar Goronyo, ya ce: “Gwamnatin Sakkwato ta kauce hanya.

“Abin da muke bukata a yanzu shi ne hanyoyin mota da magudanan ruwa. Ambaliya tana mamaye yankunan mu ne saboda babu hanya. Idan gwamnati ta kashe wannan kuɗi wajen gina hanya, sai an fi cin moriya.”

Shi ma wani Muhammad Kabiru, daga Silame, ya bayyana farin cikinsa da sayen jiragen, sai dai ya roƙi gwamnati da ta mai da hankali wajen gina hanyoyin mota saboda abin da suka fi buƙata ke nan.

“Mu a Silame jirgi yana da amfani, amma hanyar mota ita ce babbar buƙatar mu. Idan aka samar da ita, ambaliya ba za ta hana mu zirga-zirga ba.”

Yayin da gwamnatin Sakkwato ke ɗaukar matakan gaggawa don rage hatsarurruka da ambaliya ke haifarwa, al’umma na ci gaba da neman tsarin da zai magance tushen matsalar – musamman samar da ingantattun hanyoyi da magudanan ruwa a karkara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Chadi:  Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa  damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin