Hezbollah, ta yi tir da Isra’ila kan kisan gillar da aka wani babban jigonta
Published: 23rd, April 2025 GMT
Kungiyar Hezbollah, ta Lebanon ta yi tir da kakkausan lafazi da kisan da gillar da Isra’ila ta yi wani jigonta Sheikh Hussein Atoui, wanda ya yi shahada a ranar Talata, yayin wani hari da jiragen yakin Isra’ila a kusa da garin Damour na birnin Beirut.
Shugaban ofishin hulda da muslunci na kungiyar Hizbullah Sheikh Abdul Majid Ammar ya yi kakkausar suka dangane da kisan gillar dan gwagwarmayar, yana mai cewa abin takaici ne da makiya Isra’ila suka yi.
Sheikh Hussein Atoui shi ne shugaban Dakarun Al-Fajr, reshen Jamaa Islamiya (Kungiyar Musulunci) masu dauke da makamai, dake kawance da kungiyar Hamas.
Shugaban ofishin hulda da muslunci na kungiyar Hizbullah ya yi kira ga gwamnatin Lebanon da ta dauki matakai masu nagarta don kawo karshen ta’asar Isra’ila.
Babban jami’in kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon ya ce “Ya zama wajibi gwamnati ta wuce matsayin mai sa ido kawai, ta nisanci takaita kanta ga kalaman tofin Allah tsine ba tare da wani sakamako na hakika ba, sannan kuma ta dauki matakai masu tsanani, na gaggawa kuma masu tasiri a dukkan matakai da kuma hanyoyin da ake da su.”
A ‘yan watannin nan gwamnatin Isra’ila ta tsananta kashe-kashen da take yi a kasar Lebanon, inda ta karya yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka cimma a watan Nuwamban bara.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya
Majalisar Shari’ar Musulunci ta Najeriya ta naɗa Sheikh Bashir Aliyu Umar a matsayin shugabanta bayan rasuwar Sheikh AbdulRasheed Hadiyyatullah.
Wata sanarwa da majalisar ta fitar a yau Laraba ta ce an amince da shuagabancin Dokta Bashir ne kai-tsaye saboda kasancewarsa mataimakin shugaba.
A ranar Litinin ne Sheikh Hadiyyatullah ya rasu yana da shekara 81 a Jihar Osun.
“Nan gaba za a sanar da mataimakin shugaban,” in ji sanarwar da Nafiu Baba Ahmed ya sanya wa hannu a matsayin sakataren majalisar.
Sheikh Bashir sanannen malami ne kuma shi ne babban limamin masallacin Juma’a na Al-Furqan da ke Alu Avenue a Unguwar Nasarawa ta Jihar Kano.