Aminiya:
2025-07-26@08:08:03 GMT

CONMEBOL ta buƙaci a faɗaɗa Gasar Kofin Duniya ta 2030

Published: 23rd, April 2025 GMT

Hukumar Ƙwallon Ƙafar Kudancin Amurka (Conmebol) ta gabatar da buƙata a hukumance ta ƙara yawan ƙasashen da za su halarci Gasar Kofin Duniya ta 2030 zuwa ƙasashe 64.

Haɗakar ƙasashen Sifaniya da Morocco da Portugal ne za su karɓi baƙuncin gasar, bayan buɗe ta a ƙasashen Argentina da Paraguay da kuma Uruguay.

Matar da aka haifa ‘babu mahaifa’ ta haihu Abubuwa 5 da ya kamata ku sani kan mutuwar Fafaroma Francis

Gasar Kofin Duniya ta 2026 ce ta farko da ƙasashe 48 za su halarta, to amma Conmebol na son a faɗaɗa gasar ta 2030 domin murna cika shekara 100 da fara gasar.

“Hakan zai bai wa ƙasashen duniya damar kallon gasar, don haka ba wanda za a bari a baya dangane da bikin da za a yi na cika shekara 100 da fara gasar,’’ a cewar Shugaban Conmebol, Alejandro Dominguez a wani taro da hukumar ta gudanar makon jiya.

“Mun yarda cewa bikin cika shekara 100 na gasar zai zama ƙasaitacce, saboda ba a taɓa yin irin sa ba’’, in ji shi.

Shugaban Hukumar Kwallon Kafar Uruguay, Ignacio Alonso ne ya fara gabatar da buƙatar a lokacin taron FIFA da aka gudanar a cikin watan Maris.

Cikin wata sanarwa da hukumar FIFA ta fitar ta ce, haƙƙinta ne ta yi nazarin kowace shawara da mambobinsu suka gabatar.

Shugaban Hukumar ta FIFA ta, Gianni Infantino ya halarci taron Conmebol na ranar Alhamis, inda kuma ya bayyana cewa, Gasar 2030 za ta zama ‘’gagaruma’’ da ba a taɓa gani ba.

A shekarar 2017 aka ɗauki matakin faɗaɗa ƙasashen da za su halarci gasar 2026 zuwa 48 bayan duka mambobin FIFA sun kaɗa ƙuri’ar amincewa da matakin.

A ranar 15 ga watan Mayu mai zuwa ne za a gudanar da taron FIFA na 75, kuma a nan ne za a tattauna buƙatar ta Conmebol.

Idan har aka amince da buƙatar, gasar ta 2030 za ta ƙunshi karawa 128, daga karawa 64 da ake yi tsakanin 1998 zuwa 2022.

Masu sukar matakin dai na cewa, faɗaɗa gasar zai rage darajar tsarin da ake bi wajen tantance cancantar shiga gasar, yayin da Kungiyar Kare Muhalli ta FFF ta ce, shawarar buga gasar a nahiyoyi uku “barazana ce ga muhalli”.

Tuni dai a farkon watan nan Shugaban Hukumar Kwallon Kafar Turai, Aleksander Ceferin ya bayyana matakin a matsayin ‘’mummunar shawara’’.

“Wannan shawara ta yiwu ta fi ba ni mamaki fiye da ku, ni ina ganin wannan shawara ce maras kyau a ra’ayima,” in ji Ceferin a wani taron manema labarai.

Za dai a fara gasar 2030 a Uruguay – ƙasar da ta fara lashe gasar a 1930, a wani ɓangare na bikin cika shekara 100 da fara gasar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kofin Duniya cika shekara 100 a fara gasar

এছাড়াও পড়ুন:

Ɓullar Kwalara: Mutum 13 sun mutu sama da 236 na jinya a Neja

An samu ɓarkewar cutar amai da gudawa wato kwalara a ƙananan hukumomi shida na Jihar Neja, inda rahotanni suka ce mutum 13 ne suka mutu tare da wasu mutane sama da 236 da ke jinya a asibiti.

An fara samun ɓullar cutar ne a Ƙaramar hukumar Shiroro tun a ranar Lahadin da ta gabata zuwa Ƙananan hukumomin Bosso da Minna da Magama da Bida da Munya, inda jami’an kiwon lafiya suka tabbatar da ƙaruwar ɓullar cutar a ƙananan hukumomin da abin ya shafa.

Jirgin Rasha mai dauke da mutum 50 ya yi hatsari a China Matar aure ta kashe mijinta a kan abinci a Yobe

Majiyoyi sun bayyana cewa, yankunan Chanchaga a Minna da Bosso da Shiroro na daga cikin yankunan da lamarin ya fi ƙamari, lamarin da ya sa gwamnatin jihar ta ɗauki matakin gaggawa na kiwon lafiya.

Kwamishinan lafiya a matakin farko, Dakta Ibrahim Dangana, ya tabbatar da ɓullar cutar, ya kuma ce jihar ta ɗauki matakai da dama domin daƙile yaɗuwar cutar.

A cewarsa, an kafa cibiyoyin kula da lafiya da killace marasa lafiyan a kowace ƙaramar hukumar da abin ya shafa.

Dangana ya ce “Mun kafa cibiyoyin kulawa da killace masu jinya don rage yaɗuwar cutar, kuma muna kuma wayar da kan jama’a kan cutar,” in ji Dangana.

Ya ƙara da cewa, “Shirin wayar da kan jama’a ya shafi Ƙungiyoyin addini irin su Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN), kungiyoyin Islama, da masarautu takwas da ke jihar”.

Domin ƙarfafa ƙoƙarin hana yaɗuwar cutar, gwamnatin jihar ta buɗe cibiyar killacewa a tsohon reshen cibiyar kula da lafiya na matakin farko na Marigayi Sanata Idris Ibrahim Kuta daura da tsohon titin filin jirgin sama a Minna.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka
  • Iran Da Eu Sun Fara Tattaunawa A Istambul
  • Iran Ta Jaddada Wajabcin Daukan Matakin Kawo Karshen Dakatar Da Laifukan Kisan Kare Dangi A Gaza
  • Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU
  • Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja
  • An Fara Binciken Bidiyon Ciyar Da Sojoji Garaugarau
  • Kwalara: Mutum 13 sun mutu sama da 236 na jinya a Neja
  • Ɓullar Kwalara: Mutum 13 sun mutu sama da 236 na jinya a Neja
  • Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya Ya Fara Tattaunawa kan Masifar Zirin Gaza Na Falasdinu
  • Asusun Kula Da Kananan Yara Na Majalisar Dinkin Duniya “UNICEF” Ya Yi Gargadi Kan Bala’in Jin Kai A Gaza