Aminiya:
2025-11-03@14:02:09 GMT

CONMEBOL ta buƙaci a faɗaɗa Gasar Kofin Duniya ta 2030

Published: 23rd, April 2025 GMT

Hukumar Ƙwallon Ƙafar Kudancin Amurka (Conmebol) ta gabatar da buƙata a hukumance ta ƙara yawan ƙasashen da za su halarci Gasar Kofin Duniya ta 2030 zuwa ƙasashe 64.

Haɗakar ƙasashen Sifaniya da Morocco da Portugal ne za su karɓi baƙuncin gasar, bayan buɗe ta a ƙasashen Argentina da Paraguay da kuma Uruguay.

Matar da aka haifa ‘babu mahaifa’ ta haihu Abubuwa 5 da ya kamata ku sani kan mutuwar Fafaroma Francis

Gasar Kofin Duniya ta 2026 ce ta farko da ƙasashe 48 za su halarta, to amma Conmebol na son a faɗaɗa gasar ta 2030 domin murna cika shekara 100 da fara gasar.

“Hakan zai bai wa ƙasashen duniya damar kallon gasar, don haka ba wanda za a bari a baya dangane da bikin da za a yi na cika shekara 100 da fara gasar,’’ a cewar Shugaban Conmebol, Alejandro Dominguez a wani taro da hukumar ta gudanar makon jiya.

“Mun yarda cewa bikin cika shekara 100 na gasar zai zama ƙasaitacce, saboda ba a taɓa yin irin sa ba’’, in ji shi.

Shugaban Hukumar Kwallon Kafar Uruguay, Ignacio Alonso ne ya fara gabatar da buƙatar a lokacin taron FIFA da aka gudanar a cikin watan Maris.

Cikin wata sanarwa da hukumar FIFA ta fitar ta ce, haƙƙinta ne ta yi nazarin kowace shawara da mambobinsu suka gabatar.

Shugaban Hukumar ta FIFA ta, Gianni Infantino ya halarci taron Conmebol na ranar Alhamis, inda kuma ya bayyana cewa, Gasar 2030 za ta zama ‘’gagaruma’’ da ba a taɓa gani ba.

A shekarar 2017 aka ɗauki matakin faɗaɗa ƙasashen da za su halarci gasar 2026 zuwa 48 bayan duka mambobin FIFA sun kaɗa ƙuri’ar amincewa da matakin.

A ranar 15 ga watan Mayu mai zuwa ne za a gudanar da taron FIFA na 75, kuma a nan ne za a tattauna buƙatar ta Conmebol.

Idan har aka amince da buƙatar, gasar ta 2030 za ta ƙunshi karawa 128, daga karawa 64 da ake yi tsakanin 1998 zuwa 2022.

Masu sukar matakin dai na cewa, faɗaɗa gasar zai rage darajar tsarin da ake bi wajen tantance cancantar shiga gasar, yayin da Kungiyar Kare Muhalli ta FFF ta ce, shawarar buga gasar a nahiyoyi uku “barazana ce ga muhalli”.

Tuni dai a farkon watan nan Shugaban Hukumar Kwallon Kafar Turai, Aleksander Ceferin ya bayyana matakin a matsayin ‘’mummunar shawara’’.

“Wannan shawara ta yiwu ta fi ba ni mamaki fiye da ku, ni ina ganin wannan shawara ce maras kyau a ra’ayima,” in ji Ceferin a wani taron manema labarai.

Za dai a fara gasar 2030 a Uruguay – ƙasar da ta fara lashe gasar a 1930, a wani ɓangare na bikin cika shekara 100 da fara gasar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kofin Duniya cika shekara 100 a fara gasar

এছাড়াও পড়ুন:

Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan

Jamus ta shiga sahun ƙasashen duniya da ke kiran a gaggauta tsagaita wuta a yaƙin da ke ci gaba da salwantar rayuka a ƙasar Sudan.

Sama da shekaru biyu ke nan Sudan na fama da yaƙin da ya ɗaiɗaita fararen hula baya ga asarar rayuka.

Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump

Ministan Harkokin Wajen Jamus, Johann Wadephul, ya bayyana halin da Sudan ke ciki a matsayin “mummunan bala’i,” yana mai cewa babbar matsalar jinkai ta duniya a yanzu ta tattara ne a Sudan ɗin.

A taron da aka gudanar a Bahrain, ƙasashen Birtaniya da Jordan su ma sun yi magana kan rikicin, suna kiran da a kawo ƙarshen tashin hankalin.

A ƙarshen makon da ya gabata, RSF ta kori rundunar soji daga sansanin ta na ƙarshe a yammacin Darfur.

Rahotanni daga garin El-Fasher sun bayyana cewa ana samun kashe-kashe ba tare da shari’a ba, da fyaɗe da fashi har ma da hare-hare kan ma’aikatan agaji.

Wata Kungiyar Likitoci ta MSF a ranar Asabar ta ce ana fargabar dubban fararen hula sun maƙale sannan suna cikin mummunan haɗari a birnin Al Fasher wanda ya koma hannun dakarun RSF.

Rikicin Sudan ya fara ne a watan Afrilun 2023, bayan taƙaddama ta siyasa tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan, shugaban sojin ƙasar, da Mohamed Hamdan Dagalo (Hemedti), Kwamandan RSF.

Bayanai sun ce rikicin ya samo asali ne daga saɓani kan yadda za a haɗa rundunar RSF da sojojin ƙasar bayan juyin mulkin 2021 da ya hamɓarar da gwamnatin farar hula.

Tun daga lokacin, yaƙin ya zama wani mummunan bala’i na jin kai, inda Majalisar Ɗinkin Duniya (UN) ta ce fiye da mutane miliyan bakwai sun tsere daga gidajensu, yayin da dubbai ke buƙatar taimakon gaggawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Komai zai iya faruwa a hare-haren da za mu kai Nijeriya — Trump
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Yabawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Hanyoyi A Fadin Jihar
  • Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci
  • Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan
  • Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya
  • Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar
  • Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA