Gwamnan Edo Ya Dakatar da Sarki Saboda Matsalar Tsaro A Yankinsa
Published: 22nd, April 2025 GMT
An kama shi ne sakamakon wani mummunan al’amari da ya faru kwanan nan, wanda ya yi sanadin mutuwar wani babban bafadan masarautar, John Ikhamate, lamarin da ya tayar da ƙura da kira na ganin an samu adalci.
Gwamna Okpebholo ya tabbatar wa da jama’a cewa gwamnatinsa na da niyyar yaƙar rashin tsaro a faɗin jihar, tare da ɗaukar mataki kan shugabannin al’umma da suka gaza yin abin da ya dace a yankunansu.
Ya kuma buƙaci sarakunan gargajiya da su mara wa gwamnatinsa baya wajen tabbatar da zaman lafiya da haɗin gwiwa da jami’an tsaro.
Gwamnatin jihar ta kuma buƙaci al’ummar Masarautar Uwano da su kwantar da hankalinsu tare da bin doka yayin da bincike ke gudana kan lamarin kisan.
Haka kuma ta gargaɗi duk wani shugaba da aka samu da hannu a aikata ko ɓoye laifuka zai fuskanci hukunci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Dakatarwa Matsalar Tsaro Sarki
এছাড়াও পড়ুন:
Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
Gwamna Inuwa ya kuma jaddada bukatar bin ka’idojin kariya a harkokin sufurin ruwa, inda ya yi kira ga shugabannin kananan hukumomi, da shugabannin al’umma, da direbobin kwale-kwale da hukumomin da ke da ruwa da tsaki da sauran wadanda suka dace su kara kaimi wajen ganin ana kiyaye duk ka’idojin kariya don magance sake afkuwar ibtila’in a nan gaba.
Ya umurci Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Jiha (SEMA) da Majalisar. Karamar Hukumar Nafada su bayar da duk wani tallafin da ya dace ga iyalan da abin ya shafa tare da hada hannu da hukumomin da abin ya shafa don inganta tsaro da wayar da kan al’ummomin da ke yankunan kogi.
Gwamna Inuwa Yahaya ya yi addu’a yana mai cewa “A madadin gwamnati da al’ummar Jihar Gombe, ina mika sakon ta’aziyyarmu ga iyalan mamatan tare da addu’ar Allah ya jikansu da rahama ya gafarta musu kurakuransu, ya kuma saka musu da Aljannar Firdaus”.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA