Aminiya:
2025-06-14@22:56:57 GMT

Yawan mutanen da aka kashe ya ƙari zuwa 72

Published: 22nd, April 2025 GMT

Adadin mutanen da suka mutu a hare-haren da aka kai a Jihar Binuwai ya ƙaru zuwa 72.

Adadin ya ƙaru ne bayan gano ƙarin gawarwaki 13 a ranar Litinin a ƙananan hukumomin  Ukum da Logo.Adadin ya ƙaru ne bayan gano ƙarin gawarwaki 13 a ranar Litinin a ƙananan hukumomin  Ukum da Logo.

Da farko a ranar Lahadi Gwamna Hyacinth Alia a yayin da yake jawabin Ista a wani coci, ya sanar a yayin cewa an gano gawarwaki 59.

Daga bisani aka gano ƙarin gawarwaki a cikin jejin yankunan da aka kai hare-haren.

Kakakin gwmanan jihar, Isaac Uzaan, ya bayyana cewa an gano ƙarin gawarwaki 12 a Ƙaramar Hukumar Uku sauran mutum ɗaya kuma a Logo.

Tsakanin daren ranar Alhamis da safiyar Juma’a ne kai hare-hare a ƙauyukan yankin Sankera wanda ya ƙunshi ƙananan hukumar Ukum, Logo, and Kastina-Ala.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Binuwai hare hare

এছাড়াও পড়ুন:

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa

A ranar dimokuraɗiyyar Najeriya ta 2025, Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, a ranar Alhamis, ya yi afuwa ga fursunoni 66 a babbar Cibiyar gyaran hali da ke Maiduguri.

Ziyarar da Gwamna Zulum ya kai a gidan yari a ranar 12 ga watan Yuni, 2025, ya yi amfani da ikon da sashe na 212 na kundin tsarin mulkin Najeriya ya ba wa gwamnonin jihohi, wanda ya ba da damar yin afuwa bayan ya tattauna da wata majalisar ba da shawara kan jinƙai.

12 ga Yuni: Najeriya na bikin ranar dimokuraɗiyya An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe

“Dangane da ikon da aka bani a ƙarƙashin sashe na 212 na kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya (wanda aka gyara) da kuma shawarwarin kwamitin bayar da shawara kan jinƙai, don haka na yi afuwa ga fursunoni 66 da ke babbar cibiyar gyaran hali da ke nan Maiduguri,” in ji Zulum.

Ya kuma ƙara da cewa “Na kuma mayar da hukuncin kisa zuwa ɗaurin rai-da-rai tare da rage wa wasu fursunoni hukuncin zaman gidan yari a wani ɓangare na bukukuwan murnar zagayowar Ranar Dimokuraɗiyya ta bana.”

“Bayan afuwar, Gwamna Zulum ya yi wani gagarumin tallafi ta hanyar ba da gudummawar tsabar kuɗi Naira dubu 20 ga kowanne fursunoni 1,280 da ke cikin wannan gidan gyaran.”

Don ci gaba da gudanar da bukukuwan ranar dimokraɗiyya a cibiyar, ya kuma sanar da bayar da gudummawar buhunan shinkafa 300, galan 50 na man girki, da shanu guda 5.

Da yake mayar da jawabi Kwanturolan gidan gyaran hali na jihar Borno, Ibrahim Bawa ya yaba da ziyarar da Gwamnan ya kai wanda ya ce ba a taɓa yin irinsa ba.

“Wannan shi ne irinsa na farko,” in ji shi.

Yana mai cewa, babu wani gwamnan da ya gabata da ya ziyarci wurin domin yin murna ga fursunonin, musamman waɗanda suka yi sa’ar shaƙar iskar ’yanci.

Bawa ya kuma tuno da irin karamcin da Gwamnan ya yi a baya da suka haɗa da kyaututtukan buhunan shinkafa 100, galan-gadan na man girki 25, da bijimai 10 a lokacin bikin Sallah na Eid-el-Kabir na baya, wanda ya ce duk fursunoni da ma’aikata sun ji daɗin su.

Mista Gambo Samuel, wanda aka fi sani da Sarkin Gida, kuma shugaban fursunonin, ya nuna matuƙar godiya ga Gwamna Zulum dangane da wannan alfarma da ya musu na afuwar da kuma kayan abincin da ya kawo musu tallafinsa.

Ya kuma yaba wa ƙoƙarin Gwamnan na kawo sauyi a faɗin jihar, wanda ya lura akai-akai ana jin labarin sa daga sabbin fursunonin da ke shigowa wannan cibiyar lokaci zuwa lokaci.

Baya ga ziyarar da ya kai gidan gyaran halin, Gwamna Zulum ya kuma ƙaddamar da wasu ayyukan raya    ƙasa da dama na tunawa da ranar dimokuraɗiyya a cikin birnin Maiduguri da suka shafi hanyoyin mota, ruwan sha, cibiyoyin kiwon lafiya da makamantansu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawa guda bayan kwanaki 8
  • Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa
  • An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari
  • 12 ga Yuni: Najeriya na bikin ranar dimokuraɗiyya
  • Adadin Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Kashe A AfirkaTa Kudu Ya Karu Zuwa 49
  • An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a Filato