NAJERIYA A YAU: Mene ne Matsayin Mataimakin Shugaban Ƙasa A Kundin Tsarin Mulkin Najeriya?
Published: 22nd, April 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Ko kun san tanadin da kundin tsarin mulkin ƙasa ya yi game da Ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa da ayyukansa da alhakin da ya rataya a wuyansa?
Kundin na tsarin mulkin ƙasa shi ne dai kundin dokoki mafi ƙarfi a Najeriya wanda ya ƙunshi tanade-tanade a kan dukkan al’amuran da suka shafi alhakin da ya rataya a wuyan shugabanni da ma al’ummar ƙasa.
Kuma kamar yadda ya tanadi yadda ake gudanar da dukkan al’amuran ƙasa, haka ya ayyana ƙarfin ikon da kowane shugaba yake da shi, da iyakarsa da ma yadda zai iya miƙa wannan ƙarfin iko ga wani don gudanar da ayyukansa.
NAJERIYA A YAU: Me ya sa matsalar tsaro “ta gagari gwamnati” a Najeriya? DAGA LARABA: Dalilan Ɓaraka A Tsakanin Iyayen Riƙo Da Ƴaƴan RiƙoShin wanne aiki takamaimai kundin tsarin mulki ya bai wa Mataimakin Shugaban Ƙasa?
Wannan ne batun da shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa
Ya ce kuma kayan da ake fitarwa zuwa waje waɗanda ba man fetur yanzu su kusa yin kai da kai da fetur.
Ya ƙara da cewa ajiyar kuɗaɗen ƙasar a waje ya haura kusan dala biliyan 42, daga biliyan 32 lokacin da Tinubu ya hau mulki.
Har ila yau, ya ce an biya bashin da ya haura biliyan bakwai, ciki har da miliyan 800 da ake bin jiragen saman Nijeriya.
Fadar Shugaban Ƙasa ta ce yanzu jihohi na iya biyan albashi da fansho a kan lokaci, sannan suna da rarar kuɗi don ayyukan raya ƙasa, abin da ba a saba gani ba a baya.
“Bayan shekara biyu da watanni biyar kacal a ofis, Shugaba Tinubu ya cimma abubuwa da dama. Ko da Atiku da magoya bayansa ba su yadda ba, ’yan Nijeriya suna ganin sauyin,” in ji Onanuga.
Fadar Shugaban Ƙasa ta kuma zargi Atiku da jam’iyyar PDP da yaɗa maganganun da za su kawo tashin hankali.
Ya bayyana cewa yawancin matsalolin da ake fuskanta sun samo asali ne daga rashin kyakkyawan shugabanci tun a lokacin PDP, lokacin da Atiku yake mataimakin shugaban ƙasa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp