Aminiya:
2025-06-15@20:56:15 GMT

Gaza: Isra’ila ta kashe Falasindawa 58 a awa 58

Published: 8th, April 2025 GMT

Akalla Falasdinawa 58 ne aka kashe tare da jikkata wasu 213 a cikin awa 24 da suka wuce a hare-haren da Isra’ila ta kai a Zirin Gaza.

Ma’aikatar lafiya ta yankin ta sanar cewa wasu daga cikin wadanda abin ya shafa sun makale a karkashin baraguzai da kuma kan tituna, ba za a iya isa gare su ba ta hanyar motocin daukar marasa lafiya da kuma ma’aikatan tsaron farar hula.

Isra’ila ta kashe mutane 1,449 tare da jikkata wasu 3,647 tun bayan da ta karya yarjejeniyar tsagaita wuta a ranar 18 ga Maris, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Ta kara da cewa yawan Falasdinawa da aka kashe a yakin Isra’ila a Gaza zuwa 50,810, wasu 115,688 kuma sun samu raunuka tun ranar 7 ga Oktoba, 2023.

Ya lakada wa ’yarsa duka har lahira Mali, Nijar, da Burkina Faso sun janye jakadunsu daga Algeria

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Falasdinawa Isra ila

এছাড়াও পড়ুন:

Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba

Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya ce sojojin kasar Iran ba za su sararawa gwamnatin Isra’ila ba.

Jagoran ya bayyana hakan ne a wani sakon bidiyo ga al’ummar Iran ranar Juma’a biyo bayan hare-haren wuce gona da iri da Isra’ila ta yi kan kasar wanda ya kashe fararen hula, masana kimiyya da kwamandojin soji.

Ayatullah Khamenei ya kara da cewa gwamnatin Isra’ila ba za ta kubuta daga wannan aika-aika ba, yana mai tabbatar wa al’ummar Iran cewa ba za a yi sakaci kan hakan ba.

Jagoran ya jaddada cewa muguwar gwamnatin sahyoniya ta tafka babban kuskure, sannan kuma shelanta yaki ne kan Iran.

Ayatullah Khamenei ya ci gaba da cewa: dukkanin jami’an kasar Iran da bangarori daban-daban na siyasa da kuma al’ummar Iran suna da ra’ayi daya dangane da wajabcin daukar wani mataki mai karfi wajen tunkarar gwamnatin sahyoniya ta ‘yan ta’adda.

Jagoran ya kara da cewa, bai kamata gwamnatin Isra’ila ta yi tunanin cewa ta ci bulus ba, kuma komi ya wuce.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta kai sabbin hare-hare birnin Tel Aviv da Haifa
  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Kakkabo Jiragen Yakin Isra’ila Biyu Kirar F-35
  • Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara