HausaTv:
2025-11-03@16:44:26 GMT

Adadin Shahidan Gaza Sun Kai 50,669

Published: 5th, April 2025 GMT

Ma’aikatar kiwon lafiyar Falasdinawa ta sanar da cewa adadin shahidai a yankin na Gaza sun kai 50,669, yayin da wadanda su ka jikkata su ka kai 115,225.

Dangane da rahoton akan shahidan da ake samu a kowace rana kuwa,ma’aikatar kiwon lafiyar ta Falasdinawa ta ce, a cikin sa’o’i 24 da su ka gabata an sami shahidai 60, wadanda su ka jikkata kuwa sun kai 162.

Sanarwar ta kuma kara da cewa, da akwai wani adadin na shahidai masu yawa da suke kwance a kasa, ba a iya daukarsu balle a yi musu jana’iza ba, saboda yawansu, da kuma wadu dubbai da suke a karkashin baraguzai na gidajen da makaman HKI su ka rusa da mutane a cikinsu.

 A wani labarin daga Gaza, jiragen yakin HKI sun kai hari akan wata rumfa ta raba abinci ga Falasdinawa da suke fama a yunwa, da hakan ya yi sanadiyyar shahadar mutane 3 a sansanin Khan-Yunus dake kudancin zirin Gaza.

Haka nan kuma sojojin na HKI sun kai hari akan gidajen mutane a cikin gain na Khan-Yunus da ya yi sanadiyyar shahadar muutm guda.

Wasu yankunan da ‘yan sahayoniyar su ka kai wa hare-hare sun hada  Qaizan Abu Rashwan dake kudu masu yammacin Khan-Yunus, da Hayyuz-Zaitun da kudu maso gabashin Gaza, sai kuma titin Sakkah a wannan  birni.

A gefe daya mutanen Gaza suna ci gaba da yin hijirar da aka tilasta su daga Hayyul-Shuja’iyyah, zuwa yammacin Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Turkiyye na karbar taron Kasashen Musulmi Kan Halin Da Ake Ciki A Gaza

Turkiyye na karbar bakuncin wani taron ministocin harkokin wajen kasashen musulmi kan halin da ake ciki a Gaza.

Wannan taron ya zo ne bayan makonni uku da fara aiki da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza.

A cewar Turkiyya, manufar taron ita ce taimakawa wajen mutunta yarjejeniyar tsagaita wuta da kuma sake tabbatar da rawar da take takawa a wannan batu.

Ƙasashen musulmin dake halartar taron na yau Litini a Istanbul su ne wadanda Donald Trump ya aminta dasu don tabbatar da nasarar shirin zaman lafiya na Gaza.

Ministan Harkokin Wajen Turkiyye Hakan Fidan, wanda ke karbar bakuncin takwarorinsa, ya gabatar da wannan taron a matsayin hanyar yin nazari kan aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta, samar da matakai na gaba, da kuma daidaita su kafin tattaunawa da kasashen Yamma.

Haka kuma hanya ce ga wadannan kasashen da suka fi yawan al’ummar Musulmi su nuna jajircewarsu wajen kiyaye yarjejeniyar tsagaita wuta.

Ya bayyana tsagaita wuta a matsayin mafi rauni idan aka yi la’akari da kalubalen da mataki na biyu na shirin ke fuskanta.

Mataki na biyu na shirin na Trump ya tanadi kwance damarar makamai na kungiyar Hamas, samar da rundunar sulhu, da sauransu.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Isra’ila ta aikata laifuka 194 tun bayan tsagaita wuta a Gaza November 3, 2025 Girgizar kasa ta yi ajalin gomman mutane a Afghanistan November 3, 2025 Najeriya : tun kafin kalamman Trump muka dauki matakai November 3, 2025 Sudan : Mutane 1,500 sun rasa matsugunansu sakamakon tashin hankali November 3, 2025 UNICEF Tayi Gargadi Game Da Mawuyacin Hali Da Yara Ke Ciki A Gaza November 3, 2025 Hamas Ta yi Watsi Da Zargin Da Amurka Tayi Mata Kan Batun Motocin Agaji A Gaza November 3, 2025 El-Zakzaki: Yakin Sudan Yana Kare Maslahar Kasashen Yamma ne Kawai November 3, 2025 Iran Ta Karbi Sako Kan Batun Komawa Teburin Tattaunawa Ba Kai Tsaye Ba November 3, 2025 Ministar Jin Dadin Jama’a ta Sudan: Mayakan RSF Sun Kashe Mata 300 Da Yi Wa 25 Fyade A El Fasher November 3, 2025 Pezeshkian: Bunkasa Masana’antar Makamashin Nukiliyar Iran Don Inganta Rayuwar Al’ummar Iran Ne November 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Turkiyye na karbar taron Kasashen Musulmi Kan Halin Da Ake Ciki A Gaza
  • Isra’ila ta aikata laifuka 194 tun bayan tsagaita wuta a Gaza
  • Girgizar kasa ta yi ajalin gomman mutane a Afghanistan
  • Sudan : Mutane 1,500 sun rasa matsugunansu sakamakon tashin hankali
  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
  • MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Israila Ta Kai Hari  Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A