Aminiya:
2025-06-15@21:46:22 GMT

Gwamnatin Kaduna za ta ɗauki ma’aikatan lafiya 1,800 aiki

Published: 29th, March 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Kaduna, ta sanar da shirin ɗaukar ma’aikatan lafiya 1,800 aiki don inganta tsarin Kiwon Lafiya a Matakin Farko (PHC) a faɗin jihar.

Wannan zai taimaka wajen rage matsalar ƙarancin ma’aikata da kuma inganta ayyukan kiwon lafiya a jihar.

Ƙungiyar JNI ta raba wa marayu 50 kayan Sallah a Borno An sake harbe wani ƙasurgumin ɗan bindiga a Zamfara

Kamar yadda Kwamishiniyar Lafiya, Hajiya Umma Ahmad, ta bayyana, wannan mataki zai taimaka wajen rage yawan mace-macen mata masu juna biyu da yara.

“Wannan mataki zai cike giɓin da ake da shi a cibiyoyin lafiya, domin tabbatar da samun ingantaccen kiwon lafiya ga al’ummar Kaduna,” in ji ta.

Gwamnatin jihar ta fara gyara cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko guda 255 tare da samar da kayan aiki na zamani da magunguna.

Wannan zai bayar da damar kula da cututtuka kamar su ciwon suga, hawan jini, da kuma bayar da agajin gaggawa ga mata masu naƙuda.

“Ingantaccen kiwon lafiya ba gata ba ne, haƙƙi ne,” in ji Hajiya Umma, yayin da ta ke jadadda ƙudirin gwamnatin jihar kan kiwon lafiya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Daukar aiki gwamnati Ma aikatan Lafiya kiwon lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Sakon Jagora : Isra’ila ta jira hukunci mai tsanani bayan hari kan Iran

Bayan harin da gwamnatin Sahayoniya ta kai kasarmu, Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya aike da sako ga al’ummar Iran. Ga sakon kamar haka

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai

Al’ummar Iran masu daraja!

Gwamnatin yahudawan sahyoniya ta hanyar aikata wani laifi da sanyin safiyar yau, ta sake bayyana munanan dabi’arta da fasadi.

Ta hanyar kai hari dole ne wannan ya fuskanci hukunci mai tsanani.

A wannan harin makiya, kwamandoji da masana kimiyya da dama sun yi shahada.

Wadanda suka gaje su kuma da abokan aikinsu za su ci gaba da aiki nan take akan wannan tafarki, godiya ta tabbata ga Allah.

Ta hanyar wannan danyen aiki, gwamnatin Sahayoniya ta kaddara akan ta cewa zata fuskanci martini mai radadi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna
  • Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran
  • Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu
  • Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Sakon Jagora : Isra’ila ta jira hukunci mai tsanani bayan hari kan Iran