Aminiya:
2025-06-15@19:09:55 GMT

Zan sasanta Akpabio da Natasha — Ministar Harkokin Mata

Published: 7th, March 2025 GMT

Ministar Harkokin Mata, Imaan Suleiman Ibrahim, ta yi alƙawarin sasanta Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan.

Majalisar Dattawa ta dakatar da Natasha, wadda ke wakiltar Kogi ta Tsakiya, na tsawon watanni shida bayan kwamitin Ladabtarwa da Ɗa’a ya same ta da laifin karya dokokin majalisar.

Fashewar tankar mai: Mutum 7 sun mutu, gonaki sun lalace a Neja Majalisar wakilai na shirin ƙwace rajistar jam’iyyu daga hannun INEC

Yayin da ta ke magana da manema labarai bayan taron bikin Ranar Mata ta Duniya, ministar ta bayyana takaicinta kan dakatarwar da aka yi wa Natasha.

Ta ce, “Abin takaici ne kuma bai kamata ya faru ba. A majalisa ta baya, muna da mata Sanatoci guda tara, amma yanzu huɗu ne kawai suka rage.

“Ba ma son rasa kowace mace a majalisa, sai dai mu ƙara yawansu.”

Ta kuma tabbatar da cewa ana ƙoƙarin shawo kan lamarin.

“Za mu tabbatar da cewar an samu zaman lafiya ta hanyar tattaunawa da duk masu ruwa da tsaki, tare da tabbatar da cewa an yi adalci.

“Shugaban Majalisar Dattawa da kansa ya ce a shirye suke domin a sasanta. Za mu zama masu shiga tsakani don haɗa kan ɓangarorin biyu da kuma ƙarfafa haɗin kai tsakanin maza da mata a shugabanci,” in ji ta.

Wannan dai na zuwa ne biyo bayan yadda mutane daban-daban ke tofa albarkacin bakinsu kan taƙaddamar da ta ɓarke tsakanin Natasha da Akpabio.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: cin zarafi dakatarwa Ministar Harakokin Mata zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci

Babban sakataren kungiyar Hizbullah ta Lebanon Sheikh Na’im Kassim ya yi Allawadai da harin da HKI ta kai wa Iran, wanda ya bayyana shi da cewa; Yana da hatsarin gaske, kuma ‘yan sahayoniyar sun yi hakan ne bisa cikakken goyon bayan Amurka.

Sheikh Na’im Kassim ya kuma bayyana cewa; Harin na ‘yan sahayoniya ba shi da wani dalili da ya wuce a rufe bakin gaskiya wanda yake taimakawa al’ummar Falasdinu a Gaza da ake yi wa kisan kiyashi, haka nan kuma taimakawa da goyon bayan gwgawarmayar Lebanon da dukkanin wannan yankin.

Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya kuma kara da cewa; Wannan harin da wuce gona da irin za iyi tasiri mai girma a cikin wannan yankin, sannan ya kara da cewa: Wannan harin ba zai wuce ba tare da fuskantar martani daga jamhuriyar musulunci ta Iran.

Haka nan kuma Na’im Kassim ya kara da cewa; Isra’ilawa makiya tare da Amurka ba za su taba yin tasiri akan hanyar da Iran ta zabarwa kanta ba ta gwgawarmaya ko kuma rawar da take takawa a cikin wannan yankin.

Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya ce; Hizbullah da magoya bayanta, suna ci gaba da riko da tafarkin gwagwarmaya da kuma goyon bayan jamhuriyar musulunci ta Iran wajen kare hakkokinta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna
  • Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran
  • Oman ta tabbatar da soke tattaunawar Iran da Amurka zagaye na shida
  • Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka
  • Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje