Aminiya:
2025-05-01@00:32:43 GMT

Zan sasanta Akpabio da Natasha — Ministar Harkokin Mata

Published: 7th, March 2025 GMT

Ministar Harkokin Mata, Imaan Suleiman Ibrahim, ta yi alƙawarin sasanta Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan.

Majalisar Dattawa ta dakatar da Natasha, wadda ke wakiltar Kogi ta Tsakiya, na tsawon watanni shida bayan kwamitin Ladabtarwa da Ɗa’a ya same ta da laifin karya dokokin majalisar.

Fashewar tankar mai: Mutum 7 sun mutu, gonaki sun lalace a Neja Majalisar wakilai na shirin ƙwace rajistar jam’iyyu daga hannun INEC

Yayin da ta ke magana da manema labarai bayan taron bikin Ranar Mata ta Duniya, ministar ta bayyana takaicinta kan dakatarwar da aka yi wa Natasha.

Ta ce, “Abin takaici ne kuma bai kamata ya faru ba. A majalisa ta baya, muna da mata Sanatoci guda tara, amma yanzu huɗu ne kawai suka rage.

“Ba ma son rasa kowace mace a majalisa, sai dai mu ƙara yawansu.”

Ta kuma tabbatar da cewa ana ƙoƙarin shawo kan lamarin.

“Za mu tabbatar da cewar an samu zaman lafiya ta hanyar tattaunawa da duk masu ruwa da tsaki, tare da tabbatar da cewa an yi adalci.

“Shugaban Majalisar Dattawa da kansa ya ce a shirye suke domin a sasanta. Za mu zama masu shiga tsakani don haɗa kan ɓangarorin biyu da kuma ƙarfafa haɗin kai tsakanin maza da mata a shugabanci,” in ji ta.

Wannan dai na zuwa ne biyo bayan yadda mutane daban-daban ke tofa albarkacin bakinsu kan taƙaddamar da ta ɓarke tsakanin Natasha da Akpabio.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: cin zarafi dakatarwa Ministar Harakokin Mata zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar

Ma’aikatar kiwon lafiya ta kasar Uganda ta sanar da cewa, an kawo karshen Ebola da ta bulla a kasar bayan da aka dauki kwanaki 42 ba tare da an sami mutum daya wanda ya sake kamuwa  da ita ba.

 A wani bayani da ya fito daga hukumar kiwon lafiya ta duniya ( WHO), ta bayyana cewa, a lokacin bullar cutar an  gabatar da mutane 14 masu dauke da ita, an tabbatar da 12 daga cikinsu, sai wasu biyu da ba a same ta a tare da su ba.”

Haka nan kuma hukumar lafiyar ta ce, an sami mutuwar mutane 4 daga cikin wadanda su ka kamu da cutar ta Ebola, wasu mutane 10 kuma sun warke.”

Watanni 9 da su ka gabata ne dai aka tabbatar da bullar cutar a birnin Kamfala bayan da wani mutum da yake dauke da ita ya rasu.

Dajukan da kasar ta Uganda take da su, suna a matsayin matattarar cutar ta Ebola ce, wacce a karon farko ta bulla a cikin kasar a 2000.

A yankin yammacin Afirka cutar Ebola ta kashe fiye da mutane 11,000 a tsakanin 2013 zuwa 2016.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  • Da Alamu Amurka Ta Fara Dandana Kudarta
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasu
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
  • Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar