Wani mutum ya yanke jiki ana salla a Masallaci, ya rasu a asibiti
Published: 7th, March 2025 GMT
Wani mutum mai shekara 52, Salihu Byezhe, ya yanke jiki ya faɗi yayin da ake Sallar Asuba a wani masallaci da ke ƙauyen Gudaba, a Ƙaramar Hukumar Kuje a Babban Birnin Tarayya, kuma daga baya ya rasu a asibiti.
Wani mazaunin yankin, Musa Dantani, ya ce lamarin ya faru ne a ranar Alhamis bayan Byezhe ya yi sahur, ya yi alwala, sannan ya shiga masallaci don yin Sallar Asuba.
“Yayin da ake cikin sallah, kwatsam sai ya yanke jiki, nan take wasu daga cikin masu sallah suka riƙe shi suka kuma gaggauta kai shi asibiti.
“Lokacin da suke kan hanyar zuwa asibiti yana numfashi, amma da suka isa, ya rasu,” in ji Dantani.
Likitan a asibitin ya tabbatar da rasuwar Byezhe, inda ya danganta hakan da hawan jini.
Ɗaya daga cikin ’ya’yansa, wanda ke masallaci lokacin da abin ya faru, ya raka su asibiti, kuma ya ce likita tabbatar da rasuwasa.
Daga baya an gano Byezhe yana fama da matsalar hawan jini, wanda ya tashi yayin da ake sallar.
An yi jana’izarsa da misalin ƙarfe 10:12 na safiyar ranar Alhamis bisa tanadin addinin Musulunci.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hawan Jini rasuwa yanke jiki
এছাড়াও পড়ুন:
DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
Hukumar Tsaron Farin Kaya a Nijeriya DSS, ta gurfanar da fitaccen ɗan gwagwarmayar nan, Omoyele Sowore a kotu.
A ƙunshin ƙarar da DSS ta gabatar a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta haɗa da shafukan sada zumunta na X da kuma Facebook, inda take zarginsu da ba da ƙofar aibata Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Bida Poly ta sa sojoji kula da jarrabawar ɗalibai Kukan al’umma kan lalacewar hanyar DukkuDarekan shigar da ƙara na Ma’aikatar Shari’a ta Tarayya, M.B Abubakar da wasu lauyoyi huɗu —M.E. Ernest da U.B. Bulla da C.S. Eze da kuma E.G. Orubor, ne suka shigar da ƙarar a madadin Gwamnatin Tarayya da kuma hukumar ta DSS.
DSS wadda ta kafa hujja da sashe na 24 da ke cikin kundin dokokin yanar gizo, ta ce Sowore ya yi amfani da shafukansa na dandalan sada zumunta na X da Facebook wajen wallafa wani saƙo da ke cin mutuncin Shugaba Tinubu.
Tun dai a farkon watan nan ne DSS ta buƙaci goge wani saƙo da ɗan gwagwarmayar ya wallafa wanda ta riƙa a matsayin bayanan ƙarya, cin zarafi ta yanar gizo da kalaman haddasa ƙiyayya, waɗanda kuma ta ce na iya haddasa rikici su kuma ɓata sunan Najeriya a ƙasashen waje.
Sai dai har zuwa ranar Litinin, 15 ga watan Satumba, babu wani mataki da aka ɗauka na goge saƙon da DSS ɗin ta buƙata.