Wani mutum ya yanke jiki ana salla a Masallaci, ya rasu a asibiti
Published: 7th, March 2025 GMT
Wani mutum mai shekara 52, Salihu Byezhe, ya yanke jiki ya faɗi yayin da ake Sallar Asuba a wani masallaci da ke ƙauyen Gudaba, a Ƙaramar Hukumar Kuje a Babban Birnin Tarayya, kuma daga baya ya rasu a asibiti.
Wani mazaunin yankin, Musa Dantani, ya ce lamarin ya faru ne a ranar Alhamis bayan Byezhe ya yi sahur, ya yi alwala, sannan ya shiga masallaci don yin Sallar Asuba.
“Yayin da ake cikin sallah, kwatsam sai ya yanke jiki, nan take wasu daga cikin masu sallah suka riƙe shi suka kuma gaggauta kai shi asibiti.
“Lokacin da suke kan hanyar zuwa asibiti yana numfashi, amma da suka isa, ya rasu,” in ji Dantani.
Likitan a asibitin ya tabbatar da rasuwar Byezhe, inda ya danganta hakan da hawan jini.
Ɗaya daga cikin ’ya’yansa, wanda ke masallaci lokacin da abin ya faru, ya raka su asibiti, kuma ya ce likita tabbatar da rasuwasa.
Daga baya an gano Byezhe yana fama da matsalar hawan jini, wanda ya tashi yayin da ake sallar.
An yi jana’izarsa da misalin ƙarfe 10:12 na safiyar ranar Alhamis bisa tanadin addinin Musulunci.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hawan Jini rasuwa yanke jiki
এছাড়াও পড়ুন:
An ceto mutum uku da aka yi garkuwa da su a Kebbi
Rundunar ’yan sandan Jihar Kebbi ta ce ta ceto wasu mutane uku da aka yi garkuwa da su, bayan sun yi artabu da wasu da ake zargin sun yi garkuwa da su a wani mummunan musayar wuta da aka yi a tsaunin Shanga.
Waɗanda aka yi garkuwan da su sun haɗa da: Muhammad Nasamu Namata mai shekara 25, da Gide Namata mai shekara 20 da Hamidu Alhaji Namani mai shekara 35.
INEC za ta fara rajistar ƙuri’a a ranar 18 ga Agusta Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansaninta a KebbiAn yin garkuwa da su ne a safiyar ranar 27 ga watan Yuli, 2025, lokacin da masu garkuwa da mutane ɗauke da makamai suka mamaye ƙauyen Sangara da ke Ƙaramar hukumar Shanga.
A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar, CSP Nafiu Abubakar ya fitar a ranar Juma’a, ya bayyana cewa wannan ceton ya biyo bayan ɗaukar matakin gaggawa da jami’an ’yan sanda na yankin Shanga suka ɗauka, wanda ya haɗa tawagar jami’an tsaro da suka haɗa da jami’an sojojin Najeriya, jami’an tsaro na Civil Defence da ’yan banga na yankin da mafarauta.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Rundunar ta bi sahun masu garkuwa da mutanen ne zuwa tsaunin Shanga, inda aka yi musayar wuta a tsakaninsu, musayar wutar ta sa jami’an tsaro suka yi nasara kan masu garkuwar.
Daga nan masu garkuwan suka tsere zuwa cikin daji da raunukan harbin bindiga.
“An kuɓutar da waɗanda aka yi garkuwa da su ne ba tare da wani rauni ba, a ranar Alhamis, 31 ga Yuli, 2025 da misalin ƙarfe 3:30 na rana kuma a halin yanzu suna samun kulawar likita kafin su sake haɗuwa da iyalansu.”
Ya ce, Kwamishinan ’yan sanda, CP Bello M. Sani ya yaba wa jarumtaka da ƙwarewa na rundunar, inda ya buƙaci dukkan hukumomin tsaro su ci gaba da haɗa kai. Ya nanata ƙudirin rundunar na kare rayuka da dukiyoyi a Jihar Kebbi.
Kwamishinan ya kuma yi kira ga al’ummar yankin da su sanya ido tare da kai rahoto ga jami’an tsaro mafi kusa domin ɗaukar matakin gaggawa.