Majalisar Dattawa ta dakatar da Sanata Natasha na Watanni 6
Published: 6th, March 2025 GMT
Majalisar Dattawa ta dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, na tsawon watanni shida.
Wannan hukunci ya biyo bayan amincewa da rahoton Kwamitin Ladabtarwa da Ɗa’a na Majalisar, wanda ya bincike ta kan zargin karya dokokin majalisar.
Tsarin Sufuri: Gwamnatin Kano da kamfanin Stata sun ƙulla yarjejeniya Majalisar Dattawa na shirin dakatar da Natasha na wata 6Sanata Natasha ta ƙi bayyana a gaban kwamitin a ranar Laraba, duk da gayyatar da aka yi mata domin ta kare kanta.
A sakamakon haka, majalisar ta yanke hukuncin dakatar da ita har na tsawon watanni shida.
’Yar majalisar ta shiga takun saƙa da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, kan rabon kujeru a zauren majalisar.
Haka kuma, Natasha ta zargi Akpabio da cin mutuncinta a bainar jama’a da kuma hana ta gabatar da ƙudirorinta a zauren majalisar.
Ƙin amincewarta da sabon tsarin rabon kujeru ya sa Shugaban Majalisar ya hana ta damar yin magana a zauren, wanda hakan ya haifar da saɓani a tsakaninsu.
A sakamakon haka, majalisar ta tura batun zuwa Kwamitinta na Ladabtarwa da Ɗa’a don gudanar da bincike.
A zaman kwamitin na ranar Laraba, Shugaban Kwamitin, Sanata Neda Imasuen (PDP, Edo ta Kudu), ya nuna takaicinsa kan rashin halartar Natasha.
Ya ce: “Sanata Natasha an gayyace ta zuwa wannan taro. Muna fatan za ta zo yayin da muke ci gaba da zama.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Majalisar Dattawa
এছাড়াও পড়ুন:
Fizishkiyan: Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI
Shugabgan kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan wanda ya gana da fira ministan kasar Iraqi Muahmad Shi’a Sudani a taron Doha na kasashen musulmi ya bayyana cewa; Wajibi ne kasashen musulmi su hada kai idan har suna son kawo karshen laifukan da HKI take tafkawa.
Bugu da kari, shugaban kasar ta Iran ya kuma tattaunwa wasu hanyoyin da ya kamata a yi aiki da su, matukar ana son kawo karshen ta’addancin ‘yan sahayoniya.
Shugaba Fizishkiyan ya kuma ce, laifukan da HKI take tafkawa akan fararen hula a Gaza, da kashe yara da mata ta hanyar yunwa, wani lamari ne da hankali bai iya daukarsa, kuma idan musulmi su ka hada hannu da karfe wuri daya za su kawo karshensa.
A nashi gefen Fira ministan kasar Iraki ya bayyana abinda HKI take yi da cewa, isgili ne da dokokin kasa da kasa,don haka nauyi ne da ya doru a wuyan kasashen musulmi da su yi aiki domin ganin dukar matakan da suka dace.
Haka nan kuma ya ce, taron na birnin Doha dama ce ta daukar irin wadannan matakan.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000 September 15, 2025 Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces September 15, 2025 Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar September 15, 2025 Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila September 15, 2025 Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa September 15, 2025 Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata September 15, 2025 Dakarun Sojin Yamen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ramon Na Isra’ila. September 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci