Majalisar Dattawa ta dakatar da Sanata Natasha na Watanni 6
Published: 6th, March 2025 GMT
Majalisar Dattawa ta dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, na tsawon watanni shida.
Wannan hukunci ya biyo bayan amincewa da rahoton Kwamitin Ladabtarwa da Ɗa’a na Majalisar, wanda ya bincike ta kan zargin karya dokokin majalisar.
Tsarin Sufuri: Gwamnatin Kano da kamfanin Stata sun ƙulla yarjejeniya Majalisar Dattawa na shirin dakatar da Natasha na wata 6Sanata Natasha ta ƙi bayyana a gaban kwamitin a ranar Laraba, duk da gayyatar da aka yi mata domin ta kare kanta.
A sakamakon haka, majalisar ta yanke hukuncin dakatar da ita har na tsawon watanni shida.
’Yar majalisar ta shiga takun saƙa da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, kan rabon kujeru a zauren majalisar.
Haka kuma, Natasha ta zargi Akpabio da cin mutuncinta a bainar jama’a da kuma hana ta gabatar da ƙudirorinta a zauren majalisar.
Ƙin amincewarta da sabon tsarin rabon kujeru ya sa Shugaban Majalisar ya hana ta damar yin magana a zauren, wanda hakan ya haifar da saɓani a tsakaninsu.
A sakamakon haka, majalisar ta tura batun zuwa Kwamitinta na Ladabtarwa da Ɗa’a don gudanar da bincike.
A zaman kwamitin na ranar Laraba, Shugaban Kwamitin, Sanata Neda Imasuen (PDP, Edo ta Kudu), ya nuna takaicinsa kan rashin halartar Natasha.
Ya ce: “Sanata Natasha an gayyace ta zuwa wannan taro. Muna fatan za ta zo yayin da muke ci gaba da zama.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Majalisar Dattawa
এছাড়াও পড়ুন:
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji
Adedeji ya ce har zuwa sa’o’i biyu kafin sanarwar, sunan hukumar shi ne FIRS, amma yanzu sunan ya koma NRS.
Ya bayyana cewa sabuwar hukumar ba za ta tsaya kan tattara haraji kawai ba, domin yanzu tana damar tattara sauran kuɗaɗen shiga da ba na haraji ba.
Hakazalika, za ta yi aiki cikin ’yanci tare da bin ƙa’idojin bayyanan aiki da bin diddigin nasarori.
Ya ƙara da cewa sabuwar hukumar za ta mayar da hankali sosai wajen cimma nasarori, kuma za ta yi aiki da ƙwarewa kamar yadda ake yi a sauran ƙasashen duniya.
Shi ma shugaban kwamitin gyaran haraji na fadar shugaban ƙasa, Taiwo Oyedele, ya bayyana cewa ko da kuwa doka na da kyau, idan ba a aiwatar da ita yadda ya kamata ba, ba za ta amfanar da ƙasa ba.
Ya ce yanzu shugaban ƙasa ya umarce su da su fara aiki yadda ya kamata.
Oyedele ya ja hankalin jama’a cewa wannan gyara ba zai yi nasara ba sai kowa ya bayar da gudunmawarsa.
Ya ce gwamnati kaɗai ba za ta iya aiwatar da wannan sauyi ba.
Dole ne a samu haɗin gwiwar masu ruwa da tsaki, ƙungiyoyin fararen hula, ƙwararru, da abokan hulɗar ƙasa da ƙasa.
Shugaba Tinubu tun da farko ya ce dokokin harajin an tsara su ne don gina ƙasa, tare da kawar da ɓarna da kuma bunƙasa tattalin arziƙi.
Wannan gyaran haraji yana cikin babban shirin gwamnatinsa da ke neman kyautata yanayin kasuwanci, ƙara samun kuɗaɗen shiga, da kuma ganin ci gaba ya waanzu a faɗin ƙasar.
Yanzu da aka sa ranar fara amfani da dokokin a Janairun 2026, hukumomin gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki suna da lokaci don shirya duk abin da ya kamata domin tabbatar da cewa sabbin dokokin harajin sun cika burinsu na kawo ci gaba ga ƙasa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp