Majalisar Dattawa na shirin dakatar da Natasha na wata 6
Published: 6th, March 2025 GMT
Kwamitin Majalisar Dattawa ya bayar da shawarar a dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, na tsawon watanni shida.
Kwamitin ladabtarwa da ɗa’a ne, ya bayar da shawarar biyo bayan zargin da ta yi wa Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio, kan cin zarafinta.
Sheikh Sa’idu Hassan Jingir ya rasu A yi adalci a binciken mutuwar dan kwallon Nijerirya a Uganda —Gwamnatin SakkwatoA zaman Majalisar Dattawa na ranar Alhamis, Shugaban kwamitin, Neda Imasuen, ya gabatar da rahoton kwamitin, inda ya bayyana cewa Natasha ta ƙi bayar da haɗin kai wajen binciken da aka yi.
Kwamitin ya kuma bayar da shawarar a dakatar da biyanta albashi tare da janye mata jami’an tsaron da ke kula da ita.
Rikicin ya fara ne bayan da Sanata Natasha ta zargi Akpabio da ƙin amincewa da wasu ƙudurorinta, musamman wanda ya shafi Kamfanin Ƙarafa na Ajaokuta.
Haka kuma, ta ce Akpabio ya kira ta da suna “yar kulob” a zaman Majalisar, kodayake daga baya ya ba ta haƙuri.
A martaninsa, Akpabio ya musanta dukkanin zarge-zargen, inda ya bayyana cewa yana girmama mata kuma bai aikata wani abin da bai dace ba.
Wasu Sanatoci sun samu bambancin ra’ayi game da hukuncin dakatarwar.
Sanata Abba Moro daga Benuwe ta Kudu, ya bayar da shawarar a rage wa’adin dakatarwar zuwa watanni uku kawai, yayin da wasu ke goyon bayan hukuncin watanni shida.
Yanzu Majalisar Dattawa za ta tattauna kan rahoton kwamitin domin yanke hukunci na ƙarshe.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: cin zarafi dakatarwa Kwamiti Majalisar Dattawa zargi Majalisar Dattawa
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Lebanon Aun Ya Ce Mun Aike Wa Amurka Sakwanni Akan Dakatar Da Hare-haren HKI
Shugaban kasar Lebanon wanda ya gabatar da jawabi da safiyar yau ya ce; A cikin sakwannin da mu ka aike wa Amurka, mun bukaci ganin an kawo karshen hare-haren da Isra’ila take ci gaba da kawo wa Lebanon, ta sama, kasa da ruwa, haka nan kuma kisan gillar da take yi wa mutane a cikin kasar.”
Shugaba Aun ya kuma yi jinjina ga dukkanin shahidan kasar da su ka kwanta dama saboda kare Lebanon,kuma yana a matsayin wani abu ne mai kima da daraja a wurinmu.”
Shugaba Aun na Lebanon ya kuma ce, Isra’ila abokiyar gaba ce wacce take hana mutanen da yaki ya tarwatsa komawa zuwa garuruwansu da kuma sake gina kudancin Lebanon da yaki ya rusa.”
Haka nan kuma ya ce , sojojin Lebanon sun sadaukar da kawukansu ta hanyar kasancewa a tare da mutanen kudancin Lebanon.
Danagen da makaman Hizbullah, Shugaban kasar ya ce nauyi ne da ya rataya a wuyansa da kuma dukkanin ‘yan siyasa da su ga cewa makamai suna hannun gwamnati ne kadai, a hannun soja da jami’an tsaro.”
Har ila yau ya kara da cewa, yanayin da ake ciki baya da bukatuwa da duk wani abu da zai zama tsokana da tayar da hankali, ba kuma za su bari ‘yan ta’adda su cutar da al’umar Lebanon ba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sojojin Mamaya Suna Ci Gaba Da Kisan Kiyashi A Gaza July 31, 2025 Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki July 31, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata July 31, 2025 Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila July 31, 2025 Kasar Iran Ta Bayyana Gushewar Hasashen Raunin Karfin Sojinta Kuma Ba Zai Dawo Ba July 31, 2025 Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine July 31, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku July 31, 2025 Qolibaf: Barin HKI Ta Yi Abinda Taga Dama Ne Yana Karfafa Mata Giwa July 30, 2025 Yunwa Ta Kashe Karin Falasdinawa 7 A Gaza July 30, 2025 Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa July 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci