Aminiya:
2025-05-01@09:38:23 GMT

Gwamnatin Ogun ta rufe kamfanoni saboda mutuwar ma’aikata

Published: 6th, March 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Ogun ta rufe masana’antu guda biyu, na Quantum Steel Industry da ke Ogijo, a Ƙaramar Hukumar Sagamu da kuma kamfanin Xinfeng Plastics Limited da ke kan hanyar Legas zuwa Ibadan.

An rufe kamfanonin sakamakon haɗurran da ake samu a masana’antun da suka yi sanadin asarar rayuka.

An sako ɗaliban jami’ar da aka yi garkuwa da su a Binuwai An yanke wa masu fyaɗe 3 hukuncin dandanƙewa da rataya a Kaduna

An rufe kamfanin Quantum Steels saboda fashewar wani abu da ya raunata wasu ‘yan Najeriya bakwai da ma’aikata ‘yan ƙasashen waje.

Haka kuma an rufe kamfanin Xinfeng Plastics bayan da wani ma’aikacin na’ura mai suna Ishaku Monday ya rasa ransa sakamakon wutar lantarki.

Mai baiwa gwamna shawara na musamman kan Hukumar kare muhalli ta Jihar Ogun, OGEPA wanda kuma shi ne yake riƙe da matsayin shugaban kwamitin yaƙi da muhalli na jihar, Farook Akintunde ya ce gwamnati ta ɗauki matakin rufe kamfanonin ne domin gudanar da bincike kan musabbabin aukuwar lamarin cikin gaggawa da kuma samar da mafita don daƙile afkuwar lamarin nan gaba.

“A matakin gwamnati, mun ƙuduri aniyar gudanar da sahihin bincike tare da gayyato masana harkokin tsaro na waje domin gano musabbabin faruwar wannan lamari domin kare lafiyar jama’a.

“Abin da ya fi muni shi ne, duk da ziyarar da gwamnatin jihar ke kai wa waɗannan kamfanoni a kai-a kai kamar yadda sauran jihohin ke yi don wayar da kansu kan buƙatar bin ƙa’idojin tsaro, irin waɗannan al’amura sun faru a cikin gudanar da harkokin kamfanin da suke samar da su wanda ya yi sanadin asarar rayuka, don haka akwai buƙatar a rufe su,” in ji shi.

Akintunde ya ƙara da cewa kamfanonin biyu za su ci gaba da kasancewa a rufe har sai an kammala bincike tare da kafa sababbin ƙa’idojin tsaro.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Quantum Steel Industry

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Na Iran Ya Ce: Maganar ‘Yan Sahayoniyya Rudu Ne Maras Amfani

Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ya bayyana kalaman gwamnatin ‘yan sahayoniyya a matsayin wani rudu da ba shi da amfani da har zai yi tasiri a zaman tattaunawan Iran da Amurka Wanda ba na kai tsaye ba, yana mai cewa duk wani hari ko da karami ne za a kai kan Iran zai zama tamkar tartsatsin wuta da zai iya janyo tashin gobara da zai iya kona yankin gaba daya.

A jawabin da ya gabatar yayin taron kolin majalisar shawarar Musulunci ta Iran a yau Talata, Muhammad Baqir Qalibaf ya bayyana cewa: Firai ministan gwamnatin yahudawan sahayoniyya mai laifi ne mai zubar da jinin fararen hula, saboda neman hana mutuwarsa a fagen siyasa, kuma yanzu yana yin barazana ga al’ummar Iran mai girma. Qalibaf ya yi nuni da cewa, wannan mutum mai rauni yana son canza haryar tafiyarsa a kullum rana saboda tsoron kada a kama shi sakamakon kasancewarsa mai laifi da yafi zama abin ki a tarihin wannan zamani.

Qalibaf ya kara da cewa; Bayan shafe shekaru da dama Netanyahu yana yaudarar kafafen yada labarai, a halin yanzu gwamnatin yahudawan sahayoniyya ta fito fili kuma ta bayyana hakikanin fuskar wannan azzalumi ga duniya, musamman ga matasan Amurka da Turai. Qalibaf ya kara da cewa babu wani abin da wannan gwamnatin ta cimma sai kai hare-haren bama-bamai kan makarantu da asibitoci, kuma ba ta cimma burin da ta ayyana a farkon yakin ba, kuma halin da ake ciki yana da matukar rashin tabbas.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Syria: Adadin Wadanda Aka Kashe A Rikicin Bangaranci Sun Kai 70
  • Gwamnatin Tarayya ta ayyana hutu gobe Alhamis
  • An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifas
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Na Iran Ya Ce: Maganar ‘Yan Sahayoniyya Rudu Ne Maras Amfani
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
  • Shin Amurka Na Iya Komawa Kan Kadaminta A Matsayin Cibiyar Masana’antun Duniya?
  • Sin Za Ta Aiwatar Da Matakan Daidaita Samar Da Guraben Ayyukan Yi Da Raya Tattalin Arziki
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026