Gwamnatin Ogun ta rufe kamfanoni saboda mutuwar ma’aikata
Published: 6th, March 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Ogun ta rufe masana’antu guda biyu, na Quantum Steel Industry da ke Ogijo, a Ƙaramar Hukumar Sagamu da kuma kamfanin Xinfeng Plastics Limited da ke kan hanyar Legas zuwa Ibadan.
An rufe kamfanonin sakamakon haɗurran da ake samu a masana’antun da suka yi sanadin asarar rayuka.
An sako ɗaliban jami’ar da aka yi garkuwa da su a Binuwai An yanke wa masu fyaɗe 3 hukuncin dandanƙewa da rataya a KadunaAn rufe kamfanin Quantum Steels saboda fashewar wani abu da ya raunata wasu ‘yan Najeriya bakwai da ma’aikata ‘yan ƙasashen waje.
Haka kuma an rufe kamfanin Xinfeng Plastics bayan da wani ma’aikacin na’ura mai suna Ishaku Monday ya rasa ransa sakamakon wutar lantarki.
Mai baiwa gwamna shawara na musamman kan Hukumar kare muhalli ta Jihar Ogun, OGEPA wanda kuma shi ne yake riƙe da matsayin shugaban kwamitin yaƙi da muhalli na jihar, Farook Akintunde ya ce gwamnati ta ɗauki matakin rufe kamfanonin ne domin gudanar da bincike kan musabbabin aukuwar lamarin cikin gaggawa da kuma samar da mafita don daƙile afkuwar lamarin nan gaba.
“A matakin gwamnati, mun ƙuduri aniyar gudanar da sahihin bincike tare da gayyato masana harkokin tsaro na waje domin gano musabbabin faruwar wannan lamari domin kare lafiyar jama’a.
“Abin da ya fi muni shi ne, duk da ziyarar da gwamnatin jihar ke kai wa waɗannan kamfanoni a kai-a kai kamar yadda sauran jihohin ke yi don wayar da kansu kan buƙatar bin ƙa’idojin tsaro, irin waɗannan al’amura sun faru a cikin gudanar da harkokin kamfanin da suke samar da su wanda ya yi sanadin asarar rayuka, don haka akwai buƙatar a rufe su,” in ji shi.
Akintunde ya ƙara da cewa kamfanonin biyu za su ci gaba da kasancewa a rufe har sai an kammala bincike tare da kafa sababbin ƙa’idojin tsaro.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Quantum Steel Industry
এছাড়াও পড়ুন:
Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki
Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH) ya roƙi Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na KEDCO ya gaggauta dawo masa da wuta bayan rasuwar wasu marasa lafiya da ke samun kulawa ta ceton rayuwada na’ura.
Wata sanarwa da kakakin asibitin, Hauwa Inuwa Dutse ta fitar ta nuna takaici bisa rasuwar marasa lafiyan, tana mai cewa mace-macen waɗanda za a iya kauce wa ne idan akwai tsayayyiyar wutar lantarki.
Ta bayyana cewa Asibitin yana AKTH yakan biya kuɗin wuta akai-akai daga kuɗaɗen shigansa, kuma yana kashe kuɗaɗe wajen sanya mai a janareto domin amfani idan aka ɗauke wuta daga KEDCO.
Don haka, “Hukumar gudanarwar Asibitin AKTH na roƙon Kamfanin KEDCO da ya taimaka wa ayyukan asibitin ta hanyar dawo da wutar a yayin da muke ƙoƙarin biyan ragowar kuɗin wutar,” in ji sanarwar.
Ambaliya: An gano gawar ’yar shekara 3 da ruwa ya tafi da ita a Zariya Gwamnati ta gargaɗi jihohi 11 kan yiwuwar afkuwar ambaliya a wannan makonTa bayyana cewa a yayin da take ƙoƙarin biyan bashin da kamfanin ke bin sa, yana da muhimmanci a fahimci cewa yanke wutar lantarki daga muhimmiyar cibiyar lafiya babbar barazana ce ga majinyata da danginsu.