Aminiya:
2025-08-01@01:19:00 GMT

Babu abin da zai hana mu zama jam’iyya ɗaya da Kwankwaso — Shekarau

Published: 5th, March 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Kano, Mallam Ibrahim Shekarau, ya musanta cewa akwai wata ƙullaliyar gaba tsakaninsa da tsohon Gwamna Rabi’u Musa Kwankwaso, inda ya bayyana cewa babu ɗaya daga cikinsu da za a iya ɗora wa alhakin haddasa saɓanin siyasar da ya shiga tsakaninsu a baya.

Cikin wani bidiyo da karaɗe dandalan sada zumunta, Shekarau ya bayyana cewa rashin jituwar da ke tsakaninsu na siyasa ya samo asali ne daga yanayi da ya fi ƙarfinsu gaba ɗaya.

“Gaskiya ni na yi imanin cewa ni da Kwankwaso ba mu da wata matsala ta zama tare a ƙarƙashin inuwar jam’iyya ɗaya. A duk abubuwan da suka faru, da ni da shi duk babu mai laifi,” inji shi.

Da yake tsokaci kan lokacin da suka yi a jam’iyyun siyasa daban-daban, ya buga misali da yadda Kwankwaso a matsayinsa na Gwamnan Kano ya bi sahun wasu gwamnonin jihohin Sakkwato da Adamawa da Ribas wajen sauya sheƙa daga PDP zuwa APC.

Sai dai Shekarau ya bayyana cewa shugabannin riƙon kwarya na APC a wancan lokacin da suka haɗa da Bisi Akande, Muhammadu Buhari, da Bola Tinubu, sun kasa tabbatar da adalci a tsarin jam’iyyar.

“A Kano jam’iyyar ANPP ce ta kafa kashi 80 cikin 100 na jam’iyyar APC, amma saboda kasancewar shi [Kwankwaso] gwamna mai ci sai suka ware masa kashi 60 cikin 100 na shugabancin jam’iyyar, wanda muka ɗauki hakan a matsayin rashin adalci,” in ji Shekarau.

Da yake buga wani misalin, Sanata Shekarau ya ce “akwai cin fuska idan ka je sabon gidan da wasu suka gina babu gudunmawarka, ka tarar da mazauna a gidan, sai ka nemi ka yi babakere ta dole sai an ba ka ɗakin da kake so, saboda haka wannan ba abu ne mai yiwuwa ba. Shi ya sa muka ƙi goyon bayan irin wannan rashin adalci,” inji shi.

Ya ƙara bayar da misali da irin abin da ya faru a jam’iyyar PDP, yana mai cewa “a can ma Kwankwaso ba shi ne abin zargi ba, domin shugabannin jam’iyyar ne suka yanke shawara.”

A cewarsa, “ko wannan batu na rashin adalci da ya taso a jam’iyyar NNPP a yanzu, yana da nasaba ne da watsi da tsarin raba madafun iko da aka amince da shi tun farko.

“Ko a yanzu ni da Kwankwaso mukan zauna mu tattauna kan wasu batutuwa. Ba mu taɓa cewa ba za mu zauna a ƙarƙashin jam’iyya ɗaya ba. Komai yana hannun Allah.

“Shekarau 20 da suka wuce, da wani zai ce maka zan zama gwamna, da ka rantse cewa ba zai yiwu ba saboda abu da mu taɓa tsammani ba—haka shi ma ya ke a wurinsa [Kwankwaso],” in ji Shekarau.

Shekarau ya nanata cewa ƙaddarar Ubangiji ta sanya da shi da Kwankwaso da Abdullahi Umar Ganduje duk suka riƙe kujerar Gwamnan Kano “ba don babu waɗanda suka fi mu cancanta sai don haka Allah Ya riga ya rubuta.

“Akwai mutane da yawa da sun fi mu ta kowane fanni na rayuwa, amma Allah Ya zaɓe mu,” in ji Shekarau .

Aminiya ta ruwaito cewa a baya-bayan nan ana ƙoƙarin ganin an haɗa kan manyan ‘yan siyasar Kano —Kwankwaso, Ganduje da Shekarau — domin ci gaban jihar.

Ko a kwanakin tsohon ɗan takarar kujerar Sanatan Kano ta tsakiya a jam’iyyar APC, Alhaji Abdulsalam Abdulkarim Zaura, wanda aka fi sani da AA Zaura, ya bayyana aniyarsa ta sasanta manyan ‘yan siyasar jihar guda uku.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Abdullahi Umar Ganduje Jihar Kano Malam Ibrahim Shekarau Rabi u Musa Kwankwaso da Kwankwaso a jam iyyar Shekarau ya

এছাড়াও পড়ুন:

ZAMFARA: APC Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Dauki Don Matsalar Tsaro Na Kara Tsananta

Jam’iyyar APC reshen jihar Zamfara, ta bayyana matukar damuwarta kan yadda matsalar tsaro ke kara ta’azzara a jihar, inda ta bayyana hakan a matsayin abin ban tsoro da rashin fahimta.

 

A wata sanarwa dauke da sa hannun sakataren yada labarai na jam’iyyar, Yusuf Idris Gusau, jam’iyyar APC ta ce yawaitar ‘yan fashi da makami, garkuwa da mutane da kashe-kashe a Zamfara ya kai matakin da ba a taba ganin irinsa ba, yayin da ta zargi gwamnatin jihar a karkashin Gwamna Dauda Lawal da nuna halin ko in kula.

 

A cewar sanarwar, jam’iyyar ta damu matuka da wani faifan bidiyo na baya-bayan nan inda aka ga sama da mutane 200 mazauna Kaura Namoda suna rokon a taimaka musu biyo bayan sace su da wasu da ake zargin ‘yan fashi ne suka yi.

 

Jam’iyyar APC ta kuma soki gwamnatin kan abin da ta bayyana a matsayin rashin mayar da martani da kuma rashin cika alkawarin da ta dauka na kare rayuka da dukiyoyi a lokacin yakin neman zabe.

 

Jam’iyyar ta tuna cewa, Gwamna Dauda Lawal ya yi kakkausar suka ga gwamnatocin baya kan rashin tsaro, ya kuma yi alkawarin kawo karshen ‘yan fashi a cikin watanni biyun farko na mulki.

 

Sai dai jam’iyyar APC ta bayyana cewa a maimakon haka lamarin ya tabarbare, inda a kullum ake ta yin garkuwa da mutane da kashe-kashe a sassan jihar.

 

Sanarwar ta kuma bayyana wasu muhimman hanyoyi da suka hada da Gusau –Talata Mafara –Tureta, da Mayanchi –Anka –Gummi – wadanda a yanzu suke da hatsarin tafiya ba tare da rakiyar sojoji ba.

 

Jam’iyyar ta kara da cewa, hanyar Gusau zuwa Kaura Namoda ta zama daya daga cikin mafi hadari, inda a kullum ake samun rahotannin sace-sacen mutane da kashe-kashe.

 

Da take ba da misalin harin baya-bayan nan da aka ce an kashe mutane 38 da aka yi garkuwa da su daga unguwar Banga da ke karamar hukumar Kaura Namoda bayan an biya kudin fansa, jam’iyyar APC ta ce gwamnatin jihar ta yi shiru duk da cewa ana ci gaba da samun tashin hankali a tsakanin mazauna yankin.

 

A yayin da wasu sabbin rahotanni suka ce an sace sama da mutane 200 a cikin makon nan, jam’iyyar APC ta sake yin kira ga gwamnatin tarayya da ta kafa dokar ta-baci a Zamfara domin ba da damar aikewa da karin sojoji da kuma aiwatar da sahihin matakan tsaro.

 

Jam’iyyar ta zargi gwamnatin jihar da gazawa yadda ya kamata ga hukumomin tsaro na tarayya tare da zargin gwamnan da wasu mataimakansa kan harkokin yada labarai sun fito fili suna sukar ayyukan sojoji a jihar.

 

“Haka zalika ta yi Allah-wadai da rufe kasuwanni da hana zirga-zirgar ababen hawa, inda ta bayyana su a matsayin matakan da ba su da inganci da suka yi illa ga tattalin arzikin jihar.

 

Jam’iyyar APC ta kuma yi kakkausar suka kan tafiye-tafiyen da Gwamna Lawal ya yi a kasashen waje, inda ta yi zargin cewa yana halartar bukukuwan ‘yan uwa na kashin kansa yayin da mazauna gida ke kokawa da rashin tsaro.

 

Jam’iyyar ta yabawa bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara karkashin jagorancin Bashar Aliyu Gummi bisa jajircewar da ta yi wajen ganin ta yi wa bangaren zartarwa hukunci kan al’amuran da suka shafi rashin tsaro da cin hanci da rashawa.

 

A karshe jam’iyyar APC ta jajantawa iyalan wadanda rikicin ya shafa tare da yin addu’ar Allah ya dawo mana da zaman lafiya a jihar Zamfara da Najeriya baki daya.

 

REL/AMINU DALHATU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Peter Obi zai lashe jihohin Arewa idan ya koma PDP – Jerry Gana
  • 2027: Ba Mu Kafa Haɗakarmu Don Cika Burin Atiku Ba – ADC
  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 
  • ZAMFARA: APC Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Dauki Don Matsalar Tsaro Na Kara Tsananta
  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso
  •  Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta
  • Wakilin Gidan Talabijin Na Al-Alam Ya Bayyana Yadda Shi Da Iyalansa Suka Rayu Kwanaki Biyu Babu Abinci A Gaza