Karamar Hukumar Malam Madori Ta Gargadi Malaman Da Ba Sa Zuwa Aiki
Published: 3rd, March 2025 GMT
Karamar hukumar Malam Madori da ke jihar Jigawa, ta yi barazanar daukar matakin hukunta malaman makaranta da ba sa zuwa aiki.
Shugaban karamar hukumar, Alhaji Salisu Sani Garun-Gabas ya bayyana haka a wata hira da manema labarai bayan raba kudi dubu hamsin a matsayin tallafin karatu ga dalibai ashirin da biyar a yankin.
A cewarsa, wani bincike da aka gudanar bayan hawansa karagar mulki, ya nuna cewa malaman makarantu da dama ba kasafai suke zuwa aiki ba.
Ya ce hakan na daga cikin dalilan tabarbarewar ilimi a yankin, wanda ke bukatar kulawar gaggawa.
Alhaji Salisu Sani Garun-Gabas ya yi nuni da cewa, “Ilimi muhimmin abu ne a kowane fanni na rayuwar dan Adam, don haka ba za mu yi kasa a gwiwa ba wajen hukunta duk wani malamin da ba ya zuwa makaranta”.
Ya yi nuni da cewa, akwai mutane da dama wadanda suka kammala karatu kuna ba su sami aiki ba, saboda haka za a iya daukarsu fomin maye gurbin wadanda ba sa son zuwa aiki.
Shugaban ya kuma shawarci matasan yankin da su sadaukar da kansu wajen samun ilimi mai inganci, domin cigaban rayuwarsu da kasa baki daya.
Ya kara da cewa, karamar hukumar karkashin jagorancinsa za ta ci gaba da bayar da tallafi ga ilimi, domin samar da ’ya’ya masu ilimi a nan gaba.
.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Nada Aisha Mujaddadi Sabuwar Shugabar Hukumar InvestJigawa
Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Umar Namadi, ya amince da nadin Aisha Shehu Mujaddadi a matsayin shugabar Hukumar Kula da Zuba Jari ta Jihar Jigawa (InvestJigawa).
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Sakataren Gwamnatin Jihar Jigawa, Malam Bala Ibrahim, ya fitar ga manema labarai.
Sanarwar ta ce “Aisha Mujaddadi ta samu digirinta na farko a fannin tattalin arziki a Jami’ar Maiduguri a shekarar 1996, ta kara inganta iliminta da samun digiri na biyu a fannin Gudanar da Kasuwanci (MBA) daga Jami’ar Bayero, Kano a shekarar 2011.“
Malam Bala Ibrahim ya bayyana cewa Aisha Mujaddadi ta samu gogewa na tsawon shekaru 19 a fannin aikin shawarwari na ci gaban kasa da kasa, inda ta yi aiki a kan muhimman ayyuka da shirye-shirye tare da Bankin Duniya, Ma’aikatar Harkokin Waje, Harkokin kungiyar kasashen renon Ingila da Ci Gaban Birtaniya (FCDO), da Tarayyar Turai (EU), wanda hakan ya bata kwarewar da ta dace da sabon mukaminta.
Ya kara da cewa, Aisha Mujaddadi ta kasance a cikin kwamitoci da dama a matakin jiha da na tarayya, kuma ta taba zama memba a kwamitin gudanarwa na Hukumar Tara Haraji ta Jihar Kaduna.
Sakataren Gwamnatin a jaddada cewa an yi nadin ne bisa cancanta, kwarewa da gaskiya, wanda ke nuna amincewar wannan gwamnati da kwarewar Aisha Mujaddadi.
Ya bayyana fatan cewa sabuwar Darakta Janar din za ta sauke nauyin da aka dora a kanta tare da kawo ci gaba mai ma’ana ga Jihar Jigawa.
Ya kara da cewa, nadin Aisha Shehu Mujaddadi a matsayin Darakta Janar na InvestJigawa ya fara aiki nan take.
Usman Muhammad Zaria