Miji ya amince saurayin matarsa ya tare a gidansu
Published: 3rd, March 2025 GMT
Rashin kishin wani mutum ya zama abin mamaki bayan ya bayyana cewa, yana zaune lafiya tare da matarsa da suka yi shekara uku da wani saurayinta har ma sun shigo da shi cikin gidansu.
Prince Soy, matashi mai dafa abinci a kasar Japan kuma mai amfani da intanet, wanda ke tallatawa da siyar da abincin gargajiya na kasar na okara granola a intanet, kwanan nan hankali ya koma kansa.
A ranar 8 ga Yuli, ya sanar a shafin sa na sada zumunta na kafar X cewa, matarsa Seira za ta dawo gida bayan ta shafe wata shida tana karatu a kasashen waje kuma za ta dawo tare da sabon saurayinta.
Rubutun da ya wallafa wanda aka yi ta ce-ce-ku-ce a kai ya yi saurin yaɗuwa, inda ya haifar da zazzafar muhawara game da auren Pince Soy da alaƙarta da ɗaya mutumin.
Da alama dai taƙaddamar ba ta damu mijinta na aure ba, wanda a zahiri ya rubuta ziyarar saurayin matarsa ta gajeran bidiyo da samun martani a shafukan sada zumunta da yawa.
“Matata da saurayinta za su zauna tare. Tana karatu a kasar waje kuma tana da sabon saurayi.
“Za ta dawo Japan tare da shi, kuma zai zauna tare da mu, a cewar Prince Soy, wanda ya fada wa mabiyansa a shafin X.
Ya ƙara da cewa ba shi da matsala da tsarin da ba a saba gani ba.
Ya bayyana cewa, Seira ta gaya masa cewa, tana son yin karatu a ƙasar Australia a bara, kuma ya yarda duk da cewa ya yi mamakin shawarar da ta yanke.
Ta tafi a watan Janairu 2024, kuma a watan Mayu, ta furta cewa ta haɗu da wani mutumin Japan wanda daga baya ya zama saurayinta.
Saboda Prince Soy da matarsa a baya sun yanke shawarar kasancewa cikin kyakkyawar dangantaka, ba shi da wata adawa ga sabon saurayinta.
Ya kuma bayyana sakonnin rubutu na abokantaka da ya yi musaya da saurayin matarsa da kuma kyautar Starbucks (ice cream) da ya ba shi don zagayowar ranar haihuwarsa.
“Ban taɓa haduwa da shi ba, don haka ban san abubuwan da yake so ba, kuma na yi tunanin idan na ba shi wani abu mai tsada ba zai samu natsuwa ba, don haka na ba shi wani abu karami mai aminci, kamar tikitin Starbucks,” in ji Prince Soy.
A ranar 12 ga Yuli, Soy ya wallafa bidiyon kansa yana gaisawa da Seira da saurayinta a filin jirgin sama, kuma a cikin makon da ya gabata, ya ci gaba da rubuta tsarin zaman da ba na al’adar aure ba, tare da saurayin, suna tare a gidansu.
Shi da matarsa suna kwanciya a ɗakin kwana, yayin da saurayin nata yana kwana a kan kujera.
Wani lokaci sai matarsa da saurayinta suka sami sabani, sai ya shiga don yin sulhu.
“Na gode masa da gaske lokacin da yake tallafa wa matata yayin da take cikin wahala a kasar waje,” in ji Prince Soy.
“Dole ne ya zama mutum da kowa zai yi sha’awa, ko matata ba za ta faɗa masa ba.”
Ra’ayoyin jama’a a shafukan sada zumunta game da lamarin Prince Soy sun yi ta janwo muhawara, inda wasu suka yaba da niyyarsa ta bijire wa ka’idojin zamantakewa da kuma mutunta yarjejeniyar da aka ƙulla da matarsa game da dangantakarsu da juna, yayin da wasu suka ce ba za su iya fahimtar yadda ya dace da alakar zaman soyayyar mutum uku ba, musamman ganin cewa, bai taba samun wata abokiyar zama ba tun bayan auren Seira.
Dangane da amsar tambayoyi kamar “Me ya sa kake gafarta wa matarka ta yi duk abin da take so?”, sai Prince Soy ya ce, “da farko, kalmar ‘gafara’ ba daidai ba ce.
“Matata ba ta yi laifi ba. Ina son in ga matata tana nuna abin da take so wa kanta, tana yin duk abin da ta ga dama, matar da ba ta nuna abin da take so, ba ta burge ni.”
Prince Soy ya kara da cewa, a koyaushe ya san cewa, sha’awar matarsa ita ce, “samun saurayi,” amma bai taba samun matsala da hakan ba, saboda yana farin ciki matuƙar tana farin ciki.
Ya ce, a wani ɓangare, yana jin tausayin samarin Seira, domin ba za su taɓa samun matsayinsa a cikin zuciyarta ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Australia Saurayi da saurayin
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
Hukumar Tace Fina-Finai da Dab’i ta Jihar Kano ta haramta shirya duk wata muƙabala tsakanin mawaƙan yabon Annabi (S.A.W), tare da gayyatar mawaƙa Usman Maidubun Isa da Shehi Mai Tajul’izzi su bayyana a gabanta.
Hukumar ta kuma gayyaci mawaƙan ne tare da sauran waɗanda suka jagoranci muƙabalar da fitattun mawaƙan biyu suka yi ranar Litinin, da su bayyana a gabanta cikin sa’o’i 24.
Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin TinubuHakan na zuwa ne ƙasa da kwana ɗaya bayan ɓullar wata muhawara da aka yi tsakanin Usman Maidubun Isa da Shehi Mai Tajul’izzi kuma ta karade shafukan sada zumunta, wacce hukumar ta bayyana a matsayin karya dokokin aikinta.
Shugaban hukumar, Abba El-Mustapha ne ya sanar da hakan ranar Talata, inda ya ce ɗaukar matakin wani yunƙuri ne na tabbatar da zaman lafiya, daidaito da bin doka tsakanin mawaƙan nishaɗi da na addini.
El-Mustapha, a cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar, ya kuma ce an haramta duk wata nau’in muƙabala daga mawaƙan addini a jihar ba tare da izinin hukumar ba.
A yayin da yake ƙaddamar da wani kwamitin bincike da shugaban hukumar ya naɗa karkashin Daraktan Ayyuka na Musamman a hukumar, Isah Abdullahi, El-Mustapha ya umarci waɗanda aka gayyatar da su bayyana a gaban kwamitin domin amsa tambayoyi.
Hukumar ta ce shirya irin waɗannan muhawara ba tare da izininta ba ya saɓa doka kuma zai iya jawo hukunci mai tsanani ga wanda suka karya.
Hukumar ta kuma jaddada ƙudirinta na ci gaba da kula da ayyukan mawaƙan da masu nishaɗantarwa a faɗin jihar tare da yin kira ga jama’a da su zauna lafiya sannan su ci gaba da ba ta haɗin kai a ayyukanta.