Miji ya amince saurayin matarsa ya tare a gidansu
Published: 3rd, March 2025 GMT
Rashin kishin wani mutum ya zama abin mamaki bayan ya bayyana cewa, yana zaune lafiya tare da matarsa da suka yi shekara uku da wani saurayinta har ma sun shigo da shi cikin gidansu.
Prince Soy, matashi mai dafa abinci a kasar Japan kuma mai amfani da intanet, wanda ke tallatawa da siyar da abincin gargajiya na kasar na okara granola a intanet, kwanan nan hankali ya koma kansa.
A ranar 8 ga Yuli, ya sanar a shafin sa na sada zumunta na kafar X cewa, matarsa Seira za ta dawo gida bayan ta shafe wata shida tana karatu a kasashen waje kuma za ta dawo tare da sabon saurayinta.
Rubutun da ya wallafa wanda aka yi ta ce-ce-ku-ce a kai ya yi saurin yaɗuwa, inda ya haifar da zazzafar muhawara game da auren Pince Soy da alaƙarta da ɗaya mutumin.
Da alama dai taƙaddamar ba ta damu mijinta na aure ba, wanda a zahiri ya rubuta ziyarar saurayin matarsa ta gajeran bidiyo da samun martani a shafukan sada zumunta da yawa.
“Matata da saurayinta za su zauna tare. Tana karatu a kasar waje kuma tana da sabon saurayi.
“Za ta dawo Japan tare da shi, kuma zai zauna tare da mu, a cewar Prince Soy, wanda ya fada wa mabiyansa a shafin X.
Ya ƙara da cewa ba shi da matsala da tsarin da ba a saba gani ba.
Ya bayyana cewa, Seira ta gaya masa cewa, tana son yin karatu a ƙasar Australia a bara, kuma ya yarda duk da cewa ya yi mamakin shawarar da ta yanke.
Ta tafi a watan Janairu 2024, kuma a watan Mayu, ta furta cewa ta haɗu da wani mutumin Japan wanda daga baya ya zama saurayinta.
Saboda Prince Soy da matarsa a baya sun yanke shawarar kasancewa cikin kyakkyawar dangantaka, ba shi da wata adawa ga sabon saurayinta.
Ya kuma bayyana sakonnin rubutu na abokantaka da ya yi musaya da saurayin matarsa da kuma kyautar Starbucks (ice cream) da ya ba shi don zagayowar ranar haihuwarsa.
“Ban taɓa haduwa da shi ba, don haka ban san abubuwan da yake so ba, kuma na yi tunanin idan na ba shi wani abu mai tsada ba zai samu natsuwa ba, don haka na ba shi wani abu karami mai aminci, kamar tikitin Starbucks,” in ji Prince Soy.
A ranar 12 ga Yuli, Soy ya wallafa bidiyon kansa yana gaisawa da Seira da saurayinta a filin jirgin sama, kuma a cikin makon da ya gabata, ya ci gaba da rubuta tsarin zaman da ba na al’adar aure ba, tare da saurayin, suna tare a gidansu.
Shi da matarsa suna kwanciya a ɗakin kwana, yayin da saurayin nata yana kwana a kan kujera.
Wani lokaci sai matarsa da saurayinta suka sami sabani, sai ya shiga don yin sulhu.
“Na gode masa da gaske lokacin da yake tallafa wa matata yayin da take cikin wahala a kasar waje,” in ji Prince Soy.
“Dole ne ya zama mutum da kowa zai yi sha’awa, ko matata ba za ta faɗa masa ba.”
Ra’ayoyin jama’a a shafukan sada zumunta game da lamarin Prince Soy sun yi ta janwo muhawara, inda wasu suka yaba da niyyarsa ta bijire wa ka’idojin zamantakewa da kuma mutunta yarjejeniyar da aka ƙulla da matarsa game da dangantakarsu da juna, yayin da wasu suka ce ba za su iya fahimtar yadda ya dace da alakar zaman soyayyar mutum uku ba, musamman ganin cewa, bai taba samun wata abokiyar zama ba tun bayan auren Seira.
Dangane da amsar tambayoyi kamar “Me ya sa kake gafarta wa matarka ta yi duk abin da take so?”, sai Prince Soy ya ce, “da farko, kalmar ‘gafara’ ba daidai ba ce.
“Matata ba ta yi laifi ba. Ina son in ga matata tana nuna abin da take so wa kanta, tana yin duk abin da ta ga dama, matar da ba ta nuna abin da take so, ba ta burge ni.”
Prince Soy ya kara da cewa, a koyaushe ya san cewa, sha’awar matarsa ita ce, “samun saurayi,” amma bai taba samun matsala da hakan ba, saboda yana farin ciki matuƙar tana farin ciki.
Ya ce, a wani ɓangare, yana jin tausayin samarin Seira, domin ba za su taɓa samun matsayinsa a cikin zuciyarta ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Australia Saurayi da saurayin
এছাড়াও পড়ুন:
Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe, ta tabbatar da mutuwar mutum biyar da kuma jikkatar wasu 13, sakamakon tashin wutar lantarki a unguwar Tudun-Wada, Pantami a jihar.
Wutar ta tashi ne da safiyar ranar Asabar sakamakon matsala da ta taso daga wata tiransifoma a yankin, kamar yadda kakakin ’yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi, ya bayyana.
Sojoji sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwaCikin waɗanda suka rasa rayukansu har da Babban Sakatare na Ma’aikatar Ayyuka ta Musamman ta jihar, Alhaji Muhammad Yusuf Kulani, tare da ’ya’yansa da wasu mazauna unguwar.
Marigayin shi ne shugaban ƙungiyar ƙwararrun akantoci ta Jihar Gombe (ANAN).
’Yan sanda daga ofishin Low-Cost sun isa wajen don tabbatar da tsaro da kuma kai waɗanda suka jikkata zuwa asibiti.
Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Bello Yahaya, ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan mamatan.
Ya kuma ce za su gudanar da cikakken bincike domin gano musabbabin tashin wutar da kuma ɗaukar matakan kare faruwar hakan a gaba.
Ya kuma roƙi al’umma da su kasance masu bin doka tare da bayar da haɗin kai yayin gudanar da binciken.