Aminiya:
2025-07-31@20:01:40 GMT

Hakar ma’adanai: ILO ta horas da masu ruwa da tsaki kan illar bautar da yara

Published: 3rd, March 2025 GMT

A wani yunkuri na kawo karshen bautar da kananan yara a Najeriya, Kungiyar Kwadago ta Duniya (ILO ) ta horas da masu ruwa da tsaki kan tsaron sana’o’i da kuma yakar bautar da yara a aikin hakar ma’adanai.

Kungiyar da ke kula da wurare hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba ta shirya taron ne da nufin ķarfafa guiwar masu ruwa da tsaki domin kawo karshen bautar da yara a wuraren hakar ma’adinai a jihohin Neja da Osun.

Taron da ya gudanan daga ranar 18 zuwa 27 na watan Fabarirun 2025, wakilan gwamnati da kungiyoyin ma’aikata da shuwagabannin yankunan sun hallara, inda suka tattaun kan hanyoyin kawo karshen matsalar.

Kazalika an bai wa mambobin kwamitin sanya ido kan ayyukan bautar da yara na jihohin kayan aiki da za su taimaka musu wajen sanya ido kuma da kai rahoton game da bautar a kananan yara.

Miji ya amince saurayin matarsa ya tare a gidansu Ramadan: Coci ya ciyar da Musulmi 1,000 a Kaduna

A jawabinta, Daraktan kungiyar kwadago ta Najeriya, Dakta Vanessa Phala, wacce ta samu wakilcin mai kula da ayyuka na kungiyar ACCEL Africa, Misis Celine Oni, ta jaddada cewa za a aiwatar da dokoki da tsare-tsare da za su taimaka wajen kawo karshen wannan matsala.

Kudurin karfo na shirin ACCEL Africa shi ne, aiki tare da ma’aikatun kwadago da na bunkasa ayyuka da na noma, da na ma’adanai da dai sauransu.

Na biyu shi ne, daukar mataki kan sabubban bautar da yara a wuraren haķar ma’adanai, da kuma mai da hankali kan samar da kariya da kudade da kiwon lafiya da kuma aikin yi ga matasa.

Ta jaddada cewa za a magance matsalar bautar da yara, wadda ta ce talauci da rashin samun kariya ne kan gaba wajen haifar da su.

Kwanturola na ma’aikatar kwadago da inganta aiki ta kasa ta Jihar Neja, Hauwa Zakariyya, ta ce, “samar da tsaro da kiwon lafiya hakki ne a kan kowa, kuma ba za a samu wata ci gaba ba tare da tsaro ba.

“Shi ya sa muke daukar wannan kungiya ta ACCEL Africa da muhimmanci, saboda ta mayar da hankali kan wuraren haķar ma’adanai, domin daile aukuwar irin irin abin da ya faru a yankin Kuchiko, inda aka rasa rayuka da dama ciki har da yara kanana. Mun yi imanin cewar wannan tsari zai ilimantar da masu hakar ma’adanai yadda za su kare kansu a nan gaba.”

A nasa bangaren, kwantorulan na ma’aikatar kwadago na Jihar Osun, Solomon Ayinde Alabi, ya ce, “Muna murna da samun rahoto da ke tabbatar da cewa ficewar yara daga makarantu ya ragu sosai. Wannan babban labari ne gare mu a irin wadannan yankuna”.

“Ina kira gare mu a matsayinmu na iyaye  masu kulawa, da al’umma da mu yi amfani da wannan dama da kyau wajen kara azama wajen yaki da ta’addanci, bautar da yara a yankunanmu.”

Mahalarta taron sun ziyarci wuraren haķar ma’adanai a jihohi mabambata don gano hadarin da ke tattare da wannan aiki. Wani dan shekaraa Lawali Yusuf daga cikin masu haķar ma’adanai a Korokwa da ke Minna na jihar Neja ya ce, “ina wannan aiki ne saboda iyayena ba su da karfin daukar nauyin karatuna, shi ya sa nake yi don na tara kudi na fara zuwa makaranta kamar sauran abokaina.”

A yankin Idoka da ke Osun, wani dan shekara 11, Ibrahim da ke hakar ma’adanai ya ce, “burina shi ne zama mai hakar ma’adanai idan na girma, don haka ne ma na zo nan a matsayin yaron gida. Ina so na koyi yadda ake hako zinari duk da ma dai sau da dama ana kora ta daga wurin, sai dai ina dawowa saboda muradina ke nan zama mai haķar ma’adanai.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: bauatar da kananan yara hakar ma adainai yara bautar da yara a haķar ma adanai hakar ma adanai kawo karshen

এছাড়াও পড়ুন:

Shugabannin Arewa Sun Tattauna Sabon Hanyar Ci Gaba – Minista Uba Maigari Ya Yaba

 

Ministan Ƙasa na Ci Gaban Yankuna, Uba Maigari Ahmadu, ya yaba wa ci gaba da tattaunawa tsakanin jami’an gwamnati da shugabannin arewa yana mai cewa wannan “tattaunawa ce mai tarihi kuma cike da ƙarfi,” yana nuna cewa hangen nesa na Shugaba Bola Tinubu ga Arewa ya fara samo asali kuma yana haifar da sakamako.

 

Yayin jawabi a taron gidauniyar tunawa da Sir Ahmadu Bello a rana ta biyu na zaman tattaunawa tsakanin gwamnati da alumma, ministan ya jaddada cewa wannan zama shi ne karo na farko a tarihin mulkin Najeriya inda ministoci, daraktocin hukumomi, shugabannin kwamitoci, da sauran manyan jami’an gwamnati daga Arewa suka “mika kansu don a yi musu tambayoyi” daga mutanen da suke yi wa hidima.

 

Ya ce gwamnati na da rubutattun nasarori da ake iya gani, yana bayyana wannan mataki a matsayin sabon hanya don samun amincewar jama’a, “wadanda su ne a ƙarshe suka fi rinjaye wajen zabe.”

 

Tattaunawar ta shafi fannoni da dama – tsaro na abinci, noma, ilimi, lafiya da ci gaban ababen more rayuwa – inda mahalarta suka amince cewa wadannan matsaloli suna da alaƙa sosai kuma suna bukatar kulawa cikin gaggawa.

 

Ministan ya bayyana wannan zama a matsayin “tattaunawar fannoni daban-daban don makomar Arewa,” yana mai cewa burin shi ne samar da tsare-tsare masu amfani ga birane da karkara.

 

Lokacin da aka tambaye shi yadda “hanyar gaba” za ta kasance, Ahmadu ya ce manufar gwamnati ba kawai yin magana ba ce, amma ta saurara, ta yi rubutu, kuma ta yi aiki.

 

Ya kara da cewa gwamnati na mai da hankali sosai kan batun sarƙoƙin samar da abinci, farfaɗo da noma da kare ‘yancin al’ummomin makiyaya.

 

A matsayin abin da ya kira “juyin hali,” Ahmadu ya tabbatar cewa gwamnati ta amince da karin kasafin kuɗi don shirye-shiryen ci gaban Arewa – abin da ya nuna gwamnati ba kawai alkawari take yi ba, har ma tana saka kuɗi a bayansa.

 

Sai dai ministan bai boye kalubalen da ke akwai ba, ciki har da matsin tattalin arziki, rikicin al’adu da harsuna, da ƙarin matsa lamba kan ƙasar noma saboda sauyin yanayi da yawaitar jama’a.

 

Ahmadu ya jaddada cewa wannan lokaci “sabuwar farawa” ce ga Arewa, wadda ke buƙatar haɗin kai tsakanin shugabanni, al’umma da hukumomin gwamnati.

 

Taron zai ci gaba na wasu kwanaki, inda za a gabatar da ƙarin rahotanni daga ma’aikatun gwamnati da hukumomi kamar North-East Development Commission don bayyana ci gaban ayyuka.

 

“Wannan abu ne game da gaskiya, amana, da sabuwar farawa ga Arewa,” in ji Ahmadu, yana tabbatar da cewa tattaunawar da ake yi yanzu za ta tsara makomar yankin.

 

COV: Khadija Kubau

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Horas Da Mata 600 Kan Abincin Yara Mai Gina Jiki A Jigawa
  • Gwamnatin Jigawa ta horas da malamai 20,000 fasahar sadarwar zamani
  • INEC Ta Gudanar da Taron Masu Ruwa da Tsaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi na Babura/Garki
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Shugabannin Arewa Sun Tattauna Sabon Hanyar Ci Gaba – Minista Uba Maigari Ya Yaba
  • Shugaban SUBEB Yayi Alkawarin Bayar Da Tallafin Ilimi A Jihar Nasarawa
  • Gwamnonin Nijeriya Sun Yi Ta’aziyyar Waɗanda Suka Rasu A Ambaliyar Ruwa A Adamawa
  • Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci