Aminiya:
2025-07-31@22:22:48 GMT

Sarkin Sasa ya rasu bayan shafe shekaru 125 a doron ƙasa

Published: 1st, March 2025 GMT

Allah Ya yi wa Sarkin Sasa, Alhaji Haruna Maiyasin rasuwa bayan shafe shekaru 125 a duniya.

Fadar Sarkin Sasa da ke Ibadan, babban birnin Jihar Oyo, ce ta bayar da sanarwar rasuwar Sarkin wanda ke riƙe da muƙamin Sardaunan Yamma.

HOTUNA: Gobara ta laƙume shaguna 100 a Kasuwar Sakkwato An raba wa ma’aikatan gona babura 200 a Yobe

Bayanin rasuwar Sarkin Sasa yana ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Ɗan Masanin Sasa, Alhaji Kasim Ado Yaro ya raba wa manema labarai a ranar Asabar.

Ɗan Masanin na Sasa ya ce Alhaji Maiyasin ya rasu ne a yau Asabar bayan fama da rashin lafiya a wani asibiti mai zaman kansa da ke Ibadan.

Sarkin Sasa wanda kuma yake riƙe da muƙamin Shugaban Majalisar Sarakunan Hausawa a jihohi 17 na Kudancin Nijeriya ya rasu ya bar mata 2 da ’ya’ya bakwai.

Sanarwar ta ce za a yi jana’izar Alhaji Haruna Maiyasin a gobe Lahadi.

Aminiya ta ruwaito cewa tun a shekarar 1981 ce aka naɗa Alhaji Haruna Maiyasin a matsayin Sarkin Sasa.

Wakilinmu ya ruwaito cewa wani muhimmin abu da ba za a iya mantawa da shi a tarihin marigayin ba shi ne taimakon bayin Allah da kyautar kuɗi da kayan abinci da suturu bayan aikin jagorancin jama’a da ya sanya a gaba a lokacin yana raye.

Fitowa cikin jama’a ta baya bayan nan da Sarkin Sasa ya yi ita ce lokacin da ya jagoranci manyan Fadawansa zuwa ofishin Gwamnan Jihar Oyo da ke Agodi domin yi wa Gwamna Seyi Makinde ta’aziyar rasuwar yayansa watanni biyu da suka gabata.

Aminiya ta ruwaito cewa yanzu haka Sarakunan Hausawa da Fulani na kusa da birnin Ibadan da manyan malaman Addinin Musulunci suna sun fara zaman makoki a gidan marigayin da ke Sasa zuwa gobe Lahadi da za a yi masa jana’iza.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Alhaji Haruna Maiyasin Jihar Oyo Sarkin sasa Sarkin Sasa

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri

Mahara sun kashe akalla mutane biyar a Dajin Madam da ke yankin Karamar Hukumar Alkaleri ta Jihar Bauchi.

Wannan na zuwa ne bayan a makon jiya ’yan bindiga sun kutsa kauyukan da ke kusa da garin Mansur a karamar hukumar, inda suka kashe mutane hudu, suka kwashe kayayyaki a shagunansu.

Daga bisani ’yan sanda sun sun bi su, inda suka fatattake su suka gudu zuwa cikin kungurmin Dajin Madam.

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Abdulkadir Mohammed ne ya sanar da mutuwar mutanen a yayin taron zaman lafiya da aka gudanar a garin Nahutan Darazo a kokarinsa na sasanta rikicin baya-bayan nan tsakanin manoma da makiyaya da ya yi sanadin jikkatar wassu mutane a Darazo.

Gwamnan ya kuma nuna matuqar damuwarsa kan bisa yadda mafarauta da a baya suke goyon bayan ayyukan tsaro na kare dazuzzukan jihar a yanzu haka suka shiga cikin rikici da manoma.

Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata  ’Yan sa-kai aƙalla 100 da ’yan sanda 30 sun mutu a bakin aiki a Katsina —Gwamnati

Gwamna ya ce gwamnatinsa tare da hadin gwiwar hukumomin tsaro da kungiyoyin ’yan banga sun dukufa wajen kwato dabbobin da aka sace da kuma wanzar da zaman lafiya a yankunan karkara.

Ya yaba wa mafarautan yankin bisa ci gaba da goyon bayan da suke bayarwa wajen tabbatar da kare dazuzzukan. “Kun taimaka mana wajen kare dazuzzukanmu a Toro, Ningi, Duguri, Yankari, Kirfi, ba a Darazo kadai ba.

“A ranar Litinin ne ’yan bindiga suka kashe mutane biyar a Dajin Madam, wanda ke kan iyaka da Taraba, Filato, da Bauchi-Alkaleri.

“Me ya sa ba ku taimaka mana a can ba? Muna fuskantar kalubale sosai a dazuzzukanmu. Bauchi tana da dazuzzukan sama da hekta miliyan hudu da tsaunukan da ba kowa zai iya shiga ba, sai ku.”

Gwamna Bala ya alaqanta wannan tashin hankali da kwararowar jama’a daga wasu jihohi zuwa Bauchi, tare da qaruwar yawan jama’a, lamarin da ya qara matsin lamba ga kasa da albarkatun kasa.

Yace Yan bindigan yanzu Suna cikin Jihar Taraba ne,kuma Gwamnan Taraba munyi Magana dashi zamu Yi hadin guiwar Domin a fatattakesu a wurin”

Kan rikicin manoma da makiyaya a Darazo da Sade kuma, gwamna yya kaddamar da wani babban kwamiti da zai binciki rikicin na dajin Aliya, Yautare, da Farin Ruwa na Karamar Hukumar Darazo.

Mataimakin gwamnan jihar, Muhammad Auwal Jatau, wanda kuma shi ne shugaban kwamitin ne ya kaddamar da kwamitin a gidan gwamnati da ke Bauchi, inda ya kuma bukaci ’yan kwamitin da su gudanar da ayyukansu cikin himma, adalci, da rashin son kai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sarkin Gudi na Jihar Yobe, Isa Bunuwo Ibn Khaji ya rasu
  • Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya
  • Dalilan Da Suka Sa Canada Ta Goyi Bayan Kafa Kasar Falasɗinu
  • Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5
  • Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa
  • Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu
  • Kwamitin Aikin Hajjin 2025 Na Jihar Kano Ya Kammala Rahoton Aikinsa Na Wucin Gadi
  • Gwamnatin Zamfara ta amince da naɗin sabon Sarkin Katsinan Gusau
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri
  • Gwamna Lawal Ya Naɗa Sabon Sarkin Gusau