Aminiya:
2025-06-15@06:34:00 GMT

Sarkin Sasa ya rasu bayan shafe shekaru 125 a doron ƙasa

Published: 1st, March 2025 GMT

Allah Ya yi wa Sarkin Sasa, Alhaji Haruna Maiyasin rasuwa bayan shafe shekaru 125 a duniya.

Fadar Sarkin Sasa da ke Ibadan, babban birnin Jihar Oyo, ce ta bayar da sanarwar rasuwar Sarkin wanda ke riƙe da muƙamin Sardaunan Yamma.

HOTUNA: Gobara ta laƙume shaguna 100 a Kasuwar Sakkwato An raba wa ma’aikatan gona babura 200 a Yobe

Bayanin rasuwar Sarkin Sasa yana ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Ɗan Masanin Sasa, Alhaji Kasim Ado Yaro ya raba wa manema labarai a ranar Asabar.

Ɗan Masanin na Sasa ya ce Alhaji Maiyasin ya rasu ne a yau Asabar bayan fama da rashin lafiya a wani asibiti mai zaman kansa da ke Ibadan.

Sarkin Sasa wanda kuma yake riƙe da muƙamin Shugaban Majalisar Sarakunan Hausawa a jihohi 17 na Kudancin Nijeriya ya rasu ya bar mata 2 da ’ya’ya bakwai.

Sanarwar ta ce za a yi jana’izar Alhaji Haruna Maiyasin a gobe Lahadi.

Aminiya ta ruwaito cewa tun a shekarar 1981 ce aka naɗa Alhaji Haruna Maiyasin a matsayin Sarkin Sasa.

Wakilinmu ya ruwaito cewa wani muhimmin abu da ba za a iya mantawa da shi a tarihin marigayin ba shi ne taimakon bayin Allah da kyautar kuɗi da kayan abinci da suturu bayan aikin jagorancin jama’a da ya sanya a gaba a lokacin yana raye.

Fitowa cikin jama’a ta baya bayan nan da Sarkin Sasa ya yi ita ce lokacin da ya jagoranci manyan Fadawansa zuwa ofishin Gwamnan Jihar Oyo da ke Agodi domin yi wa Gwamna Seyi Makinde ta’aziyar rasuwar yayansa watanni biyu da suka gabata.

Aminiya ta ruwaito cewa yanzu haka Sarakunan Hausawa da Fulani na kusa da birnin Ibadan da manyan malaman Addinin Musulunci suna sun fara zaman makoki a gidan marigayin da ke Sasa zuwa gobe Lahadi da za a yi masa jana’iza.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Alhaji Haruna Maiyasin Jihar Oyo Sarkin sasa Sarkin Sasa

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira da a yi koyi daga akidun dan mazan jiya, kuma jagora na gari Chen Yun, tare da kara azamar dorar da kyawawan dabi’unsa cikin himma da kwazo, don gina kasar Sin mai matukar karfi.

Shugaba Xi, wanda shi ne babban sakataren kwamitin kolin JKS, kana shugaban hukumar koli ta rundunar sojojin kasar, ya yi kiran ne a yau Juma’a, cikin jawabin da ya gabatar, yayin taron bikin murnar cika shekaru 120 da haihuwar Chen Yun, taron da ya gudana a babban dakin taruwar jama’a dake tsakiyar birnin Beijing

Shugaban na Sin ya ce, an haifi Chen a shekarar 1905, ya kuma shiga JKS a shekarar 1925. Ya kuma kasance shahararren dan gwagwarmaya a rundunar ‘yantar da al’umma kuma dattijon arziki, kana daya daga cikin kusoshin da suka kafa tsarin tattalin arziki na gurguzu na kasar Sin. Kazalika, ya kasance muhimmin memba cikin jerin shugabannin JKS zangon farko mai Mao Zedong a matsayin babban jigo, kana da shugabannin JKS zango na biyu mai Deng Xiaoping a matsayin babban jigo. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Lura Da Yanayin Bala’u
  • Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Aike Da Sako Ga Al’ummar Iran Bayan Harin Da Iran Ta Fuskanta
  • Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
  • Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
  • Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi
  • Leroy Sane ya koma Galatasaray
  • Mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu — Tinubu
  • Basaraken Da Aka Sace A Kogi Ya Kuɓuta Bayan Shafe Kwanaki 27 A Hannun ‘Yan Bindiga