Aminiya:
2025-09-18@00:55:22 GMT

Ramadan: Ga arahar kayan abinci ga rashin kuɗin saya

Published: 1st, March 2025 GMT

Saɓanin shekarun baya, azumin watan Ramadan na bana ya zo a daidai lokacin da rahotanni ke nuna cewa farashin kayan abinci na sauka a sassan Najeriya.

Kayayyakin masarufi irinsu shinkafa da wake da fulawa na daga cikin waɗanda aka fi sarrafawa a watan na Ramadan, kuma su ne masu gwaggwaɓan kaso a faɗuwar farashin.

Farashin kayan masarufi na sauka a wannan karo ne baya kimanin shekara biyu a jere suna tashi a ƙasar.

Haka kuma, ana iya cewa ’yan Najeriya sun saba ganin tashin farashin kaya, musamman na abinci, a gabnin watan Ramadan.

Duk da mutane suna nuna jin daɗinsu da saukar farashin a wannan karon, amma wasu na cewa hakan bai kawo sauƙi ga talaka ba, a wannan lokaci da aka ɗauki haramar ibadar azumi, saboda rashin kuɗi a hannun jama’a.

An ga watan Ramadan a Najeriya An kama ciyaman kan zargin badaƙalar filin N100m a Kano

Wata matar aure da Aminiya ta zanta da ita ta ce, duk saukar da farashin abinci ke yi, amma ta hatsi ake yi ba ta kayan marmari ba

Ƙarancin masu sayayya

A zagayen da Aminiya ta gudanar a Kasuwar Rimi da ke Kano, ta lura da ƙarancin masu zuwa cefanen azumi a satin jajiberan Ramadan, saɓanin lokutan baya.

Bisa al’ada dai, mata kan yi cefanen kayan abinci na musamman da ake amfani da su a watan azumi, a wasu lokutan ma, har da sabbin mazuban abin ci da sha ga mai gida.

Jiya ta fi yau

Fatima Muhammad Nasir matar aure ce mai ’ya’ya biyu a Kano, ta kuma bayyana wa Aminiya cewa a kowacce shekara idan ta zo gara bara da bana ake a kan farashin kayan abinci a Najeriya.

“A bangarena kayan abincin da suka fi muhimmanci a watan azumi su ne dankali, mai, fulawa, doya, kayan shayi, da aya, zoɓo, wake, gyadar kunu, da sauransu.

Yanzu ta hatsi ake…

“A shekarun baya ina da ƙarfin sayen su nama, kaji, kifi, da doya, da ƙwai amma a bana sai wane da wane.

“Yanzu ta hatsi ake yi ba waɗannan ba. Na baki misali shekaru biyu baya kajin da mai gidan ke saya a kan N7,000 – N11,000 a bana N25,000 zuwa N30,000 ne.

“Gyaɗar kunu a kan N5,000 muka saya kwano ɗaya, aya N1,300, Zoɓo kuma N1,000. Rabin buhun dankali shekaru biyu baya akan N10,000 ne, amma yanzu akan N30,000 ake sayar da shi.”

Ita ma Asma’u Muhammad cewa ta yi tsadar kayan abinci a bana ba kaɗan ba ne idan aka kwatanta da azumin bara.

“Akwai abubuwan da sayen su sai ka ci ka tada kai a yanzu saɓanin baya.

A da, masu girke-girke a soshiyal midiya na yin girkin da muke kallo mu kwaikwaya mu yi a namu gidan, amma yanzu ba komai ne zai yi wu ba.

Ƙalubale

Wata matsala da a azumin bara aka dinga kuka da ita ce ta tsadar ƙanƙara ba da ma ƙarancinta, inda aka dinga sayen manya a kan N500 zuwa sama, ƙanana kuma N300.

Asma’u ta ce babbar matsalar da ke kawo hakan ba ta wuce matsalar rashin wutar lantarki da ta ƙi ci taƙi cinyewa ba, amma a bana tana fatan za a samu sauyi.

“Ƙalubalen da muka fuskanta a bara shi ne tsadar ƙanƙara da rashin wuta. Mutane sun sha wahala saboda an yi rana sosai kuma sanyin da za ka sha an tsuga masa kuɗi. Amma ina fata a bana haka ba za ta faru ba.”

Ita ma Fatima ta bayyana rashin wutar a matsayin babban ƙalubale, musamman a lokutan buɗa baki da sahur.

“Haka muka dinga sahur da buɗa baki a duhu a bara, saboda rashin wuta. Allah Ya sa a bana ba haka za a yi ba.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: masarufi Ramadan kayan abinci

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote

Mai kuɗin Afrika kuma Shugaban Matatar Mai ta Ɗangote, Alhaji Aliko Ɗangote, ya zargi wasu manyan masu harkar mai da shirya maƙarƙashiya domin kashe matatarsa.

Ɗangote ya yi zargin cewa miyagun ’yan kasuwan suna ƙoƙarin kashe matatar mansa mai darajar dala biliyan 20, kamar yadda aka kashe masana’antar tufafi ta ƙasar.

Ya bayyana haka ne a ranar Litinin a Legas yayin bikin cika shekara ɗaya da fara samar da fetur a matatar, inda ya ce tafiyar ta kasance cike da ƙalubale tun daga farko.

“A gaskiya tafiyar shekara ɗaya da ta wuce ta yi mana matuƙar wuya. Mun zo mu sauya tsarin kasuwancin man ƙasa. Amma wasu na ganin mun raba su da hanayar cin abinci bakinsu,” in ji shi.

’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba

Ya ci gaba da cewa, “Amma abin da muka yi shi ne mun sa Najeriya da nahiyar Afirka gaba ɗaya su yi alfahari.”

Ɗangote ya ce matatar ta riga ta fitar da lita biliyan 1.8 na man fetur zuwa ƙasashen waje cikin watanni uku da suka gabata, sannan tana da isasshen ƙarfi wajen cika buƙatar cikin gida.

Ya ce tun daga fara aikin matatar a watan Satumbar 2024, dogayen layukan man fetur da suka fi shekaru 50 ana fama da su a Najeriya sun zama tarihi.

Ɗangote ya ƙara da cewa farashin fetur ya sauka daga kusan Naira 1,100 zuwa N841 a wasu jihohi, kuma da zarar sabbin motocin gas (CNG) masu dakon mai sun fara aiki a duk faɗin ƙasar, rage farashin zai fi tasiri.

Ya kuma bayyana cewa sabbin motocin CNG 4,000 za su samar da aƙalla ayyukan yi 24,000, ciki har da direbobi, makanikai da sauran ma’aikata.

“Ba mu kore kowa daga aiki ba, sai dai muna ƙara samar da ayyuka,” in ji shi.

Ɗangote ya zargi masu harkar mai da haɗa kai da ’yan kasuwa na cikin gida da na waje da ƙoƙarin hana nasarar matatar.

“Yadda aka hallaka masana’antar yadi, haka suke ƙoƙarin kashe matatar mu,” in ji shi.

A kan zargin cewa bai wadatar da ƙasa da fetur ba, sai ya mayar da martani da cewa: “Idan ba mu da ƙarfin samar da mai, me ya sa muke fitarwa zuwa ƙasashen waje?”

Ya kuma yi ba’a ga Ƙungiyar Ma’aikatan Mai (NUPENG) wadda ta ce rage farashin fetur na matatar Dangote “kyautar Girka ce.” Dangote ya ce: “Ko da kuwa kyautar Girka ce, ai kyauta ce, za ta kuma ci gaba da kasancewa.”

Ya jaddada cewa abin da Najeriya ke buƙata yanzu shi ne kare masana’antunta, domin ci-gaban tattalin arziki da kuma rage dogaro da shigo da kaya daga waje.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNICEF Ya Ba Da Tallafin Kayayyakin Aiki Ga Cibiyoyin Lafiya A Kirikasamma
  • Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Kundin Bajinta na Guinness ya taya Hilda Baci murna
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar