Aminiya:
2025-06-15@14:28:34 GMT

Ramadan: Ga arahar kayan abinci ga rashin kuɗin saya

Published: 1st, March 2025 GMT

Saɓanin shekarun baya, azumin watan Ramadan na bana ya zo a daidai lokacin da rahotanni ke nuna cewa farashin kayan abinci na sauka a sassan Najeriya.

Kayayyakin masarufi irinsu shinkafa da wake da fulawa na daga cikin waɗanda aka fi sarrafawa a watan na Ramadan, kuma su ne masu gwaggwaɓan kaso a faɗuwar farashin.

Farashin kayan masarufi na sauka a wannan karo ne baya kimanin shekara biyu a jere suna tashi a ƙasar.

Haka kuma, ana iya cewa ’yan Najeriya sun saba ganin tashin farashin kaya, musamman na abinci, a gabnin watan Ramadan.

Duk da mutane suna nuna jin daɗinsu da saukar farashin a wannan karon, amma wasu na cewa hakan bai kawo sauƙi ga talaka ba, a wannan lokaci da aka ɗauki haramar ibadar azumi, saboda rashin kuɗi a hannun jama’a.

An ga watan Ramadan a Najeriya An kama ciyaman kan zargin badaƙalar filin N100m a Kano

Wata matar aure da Aminiya ta zanta da ita ta ce, duk saukar da farashin abinci ke yi, amma ta hatsi ake yi ba ta kayan marmari ba

Ƙarancin masu sayayya

A zagayen da Aminiya ta gudanar a Kasuwar Rimi da ke Kano, ta lura da ƙarancin masu zuwa cefanen azumi a satin jajiberan Ramadan, saɓanin lokutan baya.

Bisa al’ada dai, mata kan yi cefanen kayan abinci na musamman da ake amfani da su a watan azumi, a wasu lokutan ma, har da sabbin mazuban abin ci da sha ga mai gida.

Jiya ta fi yau

Fatima Muhammad Nasir matar aure ce mai ’ya’ya biyu a Kano, ta kuma bayyana wa Aminiya cewa a kowacce shekara idan ta zo gara bara da bana ake a kan farashin kayan abinci a Najeriya.

“A bangarena kayan abincin da suka fi muhimmanci a watan azumi su ne dankali, mai, fulawa, doya, kayan shayi, da aya, zoɓo, wake, gyadar kunu, da sauransu.

Yanzu ta hatsi ake…

“A shekarun baya ina da ƙarfin sayen su nama, kaji, kifi, da doya, da ƙwai amma a bana sai wane da wane.

“Yanzu ta hatsi ake yi ba waɗannan ba. Na baki misali shekaru biyu baya kajin da mai gidan ke saya a kan N7,000 – N11,000 a bana N25,000 zuwa N30,000 ne.

“Gyaɗar kunu a kan N5,000 muka saya kwano ɗaya, aya N1,300, Zoɓo kuma N1,000. Rabin buhun dankali shekaru biyu baya akan N10,000 ne, amma yanzu akan N30,000 ake sayar da shi.”

Ita ma Asma’u Muhammad cewa ta yi tsadar kayan abinci a bana ba kaɗan ba ne idan aka kwatanta da azumin bara.

“Akwai abubuwan da sayen su sai ka ci ka tada kai a yanzu saɓanin baya.

A da, masu girke-girke a soshiyal midiya na yin girkin da muke kallo mu kwaikwaya mu yi a namu gidan, amma yanzu ba komai ne zai yi wu ba.

Ƙalubale

Wata matsala da a azumin bara aka dinga kuka da ita ce ta tsadar ƙanƙara ba da ma ƙarancinta, inda aka dinga sayen manya a kan N500 zuwa sama, ƙanana kuma N300.

Asma’u ta ce babbar matsalar da ke kawo hakan ba ta wuce matsalar rashin wutar lantarki da ta ƙi ci taƙi cinyewa ba, amma a bana tana fatan za a samu sauyi.

“Ƙalubalen da muka fuskanta a bara shi ne tsadar ƙanƙara da rashin wuta. Mutane sun sha wahala saboda an yi rana sosai kuma sanyin da za ka sha an tsuga masa kuɗi. Amma ina fata a bana haka ba za ta faru ba.”

Ita ma Fatima ta bayyana rashin wutar a matsayin babban ƙalubale, musamman a lokutan buɗa baki da sahur.

“Haka muka dinga sahur da buɗa baki a duhu a bara, saboda rashin wuta. Allah Ya sa a bana ba haka za a yi ba.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: masarufi Ramadan kayan abinci

এছাড়াও পড়ুন:

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

Babu abin da ya rage yanzu, illa babatun zantukan siyasa da ‘yan siyasar ke ta fama yi a kasar, wadanda suka jarabtu da matukar son mulki. Wannan abu da ke faruwa yanzu, ko shakka babu zai canja, zai canja din ne kuwa yayin da ‘yan siyasar ke aiwatar da tsare-tsarensu, sai masu jefa kuri’u a Nijeriya kuma su yanke hukunci. Shekarar 2027, za ta kasance mai ban mamaki tare da kalubale ga ‘yan Nijeriya.

A bisa dukkan alamu, jam’iyyar APC ta dukufa wajen kara habaka karfinta ne kawai da ganimar ‘yan adawa. Tana ta faman sa kanta cikin rigingimu, har wadanda ba su shafe ta ba a cikin shekaru biyun da ya rage mata ta yi gaba na kunci da tsanani. Maimakon gwamnatin ta mayar da hankali kan nauye-nauyen da ke kanta, na yi wa al’ummar kasa aiki; sai ta buge da yin fada da jam’iyyar adawa, kullum cikin wasa wukarta; a gefe guda kuma gazawar gwamnatin na fitowa fili.

Kura-kuren gwamnatin sun hada da; girman kai wajen tafiyar da al’amuranta, rashin tafiyar da abubuwa yadda ya kamata; tunanin cewa, jawo ‘yan adawa zai ba ta dama tare da karfin yin fada da kuma lashe zabe; ta hanyar zaben shugaban kasa cikin sauki, wanda kowane bangare zai bayar da gudunmawarsa. Amma, babbar matsalar ita ce; shugaban kasar ba shi da kima a kusan dukkanin sassan kasar.

Jam’iyya mai mulki, za ta iya bunkasa damar da take da ita, idan ba ta tsayar da Tinubu a 2027 ba, musamman idan za ta tsayar da matashi, lafiyayye, dan siyasa mai gaskiya da son ci gaba. Hakan kuwa, da alamu ba zai yiwu ba, domin Tinubu shi ne ked a wuka da nama a jam’iyyar.

Shugaban kasa da kansa, ba zai iya bayar da shawarar yadda za a yi gyara ta hanyar kawo wani dan takarar da ya dace ba. Idan Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, zai kasance a matsayin dan takara, APC za ta yi amfani da dukkanin damammakin da take das u, musamman na amfani da kudi wajen sayen kuri’u da masu zabe. Rage Muslman Arewa saboda Kiristocin Arewa, na iya zama hadari, amma wannan shi ne kawai abin da za a iya yi.

Haka zalika, jam’iyyar ta zama dakikiyar daliba, domin babu abin da take karantawa illa yadda za ta samu damammaki iri daban-daban na siyasa kadai. Dandazon da ‘yan siyasa suka yi a cikinta, ba karamar barazana ba ce ga masu bukatu daban-daban, musamman idan aka kasa biya musu bukatunsu.

Ko shakka babu, Arewa za ta yi matukar tasiri a zaben da za a yi. Shi ne yankin day a fuskantar ayyukan ta’addanci da kuma mummunan talauci da ke biye da su har zuwa rumfunansu na zabe. Saboda haka, dole ne jam’iyyar ta yi aiki tukur don kaucewa sake faruwar zaben 2015, lokacin da jam’iyya mai mulki ta fuskanci daukacin yankin da suka yi mata zanga-zanga.

Kudu-maso-yamma, za su iya goyon bayansa idan ya kasance manyan ‘yan adawa sun fitar da wani dan takarar daga Arewa, amma wannan rashin kwanciyar hankali da ake fama das hi, ya kamata a ce ya hana kowa barci.

Tasirin Wike, zai iya raunanawa ko karfafawa; ya danganta da matakin da ‘yan adawa suka dauka game da rikice-rikice a Kudu-maso-kudu, wanda zai iya daidai da bukatunsu; ba abubuwan da suka dace ba. Za a lalata jam’iyyar LP ba tare da Obi ba, a kuma matse shi a matsayinsa na dan takararta.

Burin Obi yanzu, ya wuce batun jam’iyyar LP; amma akwai barazanar samun raguwa a matsayinsa na dan siyasa, idan ya yanke shawarar da za ta iya raba mabiyansa. Kudu-maso-gabas, sun kagu su ga sun samu mukamin shugabancin kasa, wanda hakan ke nuna kishinta na samun daidaito. Hakan, na iya yiwuwa ta hanyar samun daidaito, ana iya samun hakan ta hanyar yarjejeniya a tsakanin yankunan da ake da su.

Da alamu dai, tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ne ke da babbar matsala. Ya yi rauni da yawa da zai iya ja da bukatar Tinubu na neman wa’adi na biyu. Don haka, sake barin jam’iyyar PDP tare da neman wata jam’iyyar daban, hanya ce kawai ta kasha makudan kudade da bata lokaci da sauran makamantansu.

PDP a halin yanzu, na zub da jini ne sakamakon zagon kasan da jam’iyya mai mulki ke yi mata. Babbar kadararta shi ne Atiku, amma kuma shi ne babbar matsalarta. Matsayinsa na farko a jam’iyyar, shi ne ke haifar da korafe-korafe da rudani, zai yi wuya PDP tare da Atiku su shiga yarjejeniyar da za ta bayar da dama a karo na biyu.

Idan da PDP za ta iya gyaruwa ta samu nasara a kan APC, dab a ta damu da neman biyan bukatun da suka fi muni ko kawo rudani ba. Jam’iyyar da ta taba yi wa al’ummar kasar barazana, yanzu kuma tana cikin sadar kafa tarihi wajen rubuta ta a matsayin wacce da fi bayar da gudunmawa wajen samun nasarar APC 2027.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 
  • Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba
  • Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci
  • Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba
  • Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya
  • Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya