Aminiya:
2025-11-02@17:17:52 GMT

Rage Albashi: Abba ya dakatar da muƙaddashin shugaban ma’aikatan Kano

Published: 28th, February 2025 GMT

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya dakatar da Muƙaddashin Shugaban Ma’aikata kuma Babban Sakataren Tsare-Tsare, Salisu Mustapha, kan badaƙalar zaftare albashin ma’aikata ba bisa ƙa’ida ba.

An umarci Mustapha da ya sauka daga muƙaminsa na Babban Sakataren Tsare-Tsare a Ofishin Shugaban Ma’aikata domin ba da damar gudanar da bincike.

A gaban mijina Akpabio ya nemi kwanciya da ni —Sanata Natasha Buhari ya koma Kaduna da zama bayan shafe shekara 2 a Daura

Gwamna Abba ya amince da naɗa Malam Umar Muhammad Jalo, Muƙaddashin Babban Sakataren REPA, a matsayin Muƙaddashin Shugaban Ma’aikatan jihar har zuwa lokacin da za a kammala binciken lamarin.

Matakin gwamna ya biyo bayan ƙorafe-ƙorafen da dama da ma’aikatan gwamnati suka yi kan rage albashi ba bisa ƙa’ida da kuma jinkirin biyan albashi a kan lokaci.

A martaninsa, ya jaddada matsayin gwamnatinsa na rashin amincewa da duk wani rashin gaskiya da suka shafi harkokin kuɗi.

Ya kuma yi alƙawarin cewa duk wanda aka samu da hannu a lamarin za a hukunta shi.

“Wannan gwamnati ba za ta lamunci duk wani zalunci a kan ma’aikata ba. Duk wanda aka kama yana wawure albashin ma’aikata za a hukunta shi ba tare da la’akari da muƙaminsa ba,” in ji Gwamna Abba.

Domin shawo kan matsalar, gwamnan ya kafa kwamitin mutum bakwai wanda Kwamishinan Raya Karkara, Abdulkadir Abdussalam, zak jagoranta.

Gwamnan ya bai wa kwamitin umarni da ya duba albashin ma’aikata daga watan Oktoban 2024 zuwa Fabrairun 2025 domin gano waɗanda abin ya shafa, tantance asarar kudade, da bayar da shawarwari kan matakin da ya dace a ɗauka.

An umarci kwamitin da kammala bincikensa cikin kwanaki bakwai tare da gabatar da cikakken rahoto.

An naɗa Salisu Mustapha a matsayin Muƙaddashin Shugaban Ma’aikatan jihar a farkon wannan wata bayan Shugaban Ma’aikata jihar, Abdullahi Musa, ya tafi hutun jinya zuwa ƙasar Indiya domin neman magani.

Gwamna Abba ya tabbatar wa ma’aikatan Jihar Kano cewa gwamnatinsa na da niyyar kasancewa adala, mai gaskiya, da kuma biyan albashi a kan lokaci.

Ya gargaɗi duk wani jami’in gwamnati da ke da hannu a badaƙalar kuɗi cewa zai fuskanci fushin doka.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya

Hukumar zaben kasar Tanzaniya ta bayyana shugabar kasa mai ci Samia Suluhu Hassan a matsayin wadda ta lashe zaben shugaban kasar.

Shugaban hukumar zaben ya ce Shugaba Samia ta yi nasara a zaben da kashi 98% na jimillar kuri’un da aka kada.

Bayanai sun ce manyan ‘yan takarar adawa ba su shiga ba, wasu kuma an tsare su ko kuma an hana su tsayawa takara, wanda hakan ya haifar da tashin hankali.

Jam’iyyar adawa ta kasar ta ce daruruwan mutane ne suka mutu sanadiyyar zanga-zangar da aka kwashe kwanaki ana yi tun bayan zaben na ranar Laraba.

Wani mai magana da yawun jam’iyyar adawa ta Chadema ya shaida wa AFP cewa kimanin mutane 700 ne suka mutu, a alkalumman da aka tattara daga asibitoci.

Gwamnatin Shugaba Samia ta musanta duk wani “yin amfani da karfi fiye da kima,” yayin da Ministan Harkokin Waje Mahmoud Thabit Kombo ya shaida wa Al Jazeera cewa babu “bayani” kan adadin wadanda suka mutu.

Hukumomin sun katse hanyar intanet, sun sanya dokar hana fita, kuma sun takaita ‘yan jarida, wanda hakan ya takaita samun bayanai.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar November 1, 2025 Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific November 1, 2025 Israila Ta Kai Hari  Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A November 1, 2025 Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci November 1, 2025 Iran Ta Sanya  Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3 October 31, 2025 Isra’ila Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza October 31, 2025 An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta October 31, 2025 M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi October 31, 2025 Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda October 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya
  • Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 
  • Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta