Boko Haram sun sace mutum 2 da kayan abinci a Borno
Published: 26th, February 2025 GMT
’Yan Ta’addan Boko Haram sun kai hari ƙauyen Kaleri da ke Ƙaramar Hukumar Jere a Jihar Borno, inda suka sace mutum biyu da kayan abinci masu tarin yawa.
Wata majiya daga yankin ta tabbatar da cewa lamarin ya faru ne kusa d Jami’ar Maiduguri (UNIMAID).
Buhari da El-Rufai ba su halarci babban taron APC ba Ƙungiya ta raba wa marayu da mabuƙata kayan makaranta a KanoMajiyar ta ce, “Sun shigo da manyan makamai, suna harbe-harbe suna bi gida-gida don neman kayan abinci, suna sanya tsoro a zukatan mazauna garin.
Wani mazaunin yankin da ya nemi a sakaya sunansa ya ce, “Sun yi garkuwa da mutane biyu, sannan suka kwashe kayan abinci.”
Bayan faruwar lamarin, jami’an ’yan sanda sun rufe yankin tare da kama wasu mutane, amma ba su bayyana cewar waɗanda suka kama na da alaƙa da harin ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram Garkuwa Kayan abinci Ƙauye kayan abinci
এছাড়াও পড়ুন:
Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar
An shiga yanayin zaman dar-dar a yankin Gabas ta Tsakiya bayan wasu munana hare-hare da Isra’ila ta kaddamar a kan tashoshin Nukiliya da manyan sojojin Iran a ranar Alhamis.
Hukumomin Isra’ila dai sun tabbatar da kai harin inda suka ce ya kunshi daruruwan jirage kan abin da suka kira da kololuwar wurin hada makaman Nukiliya na Iran da kuma manyan sojojinta.
NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a KadunaDaga cikin manyan mutanen da ake zargin harin ya hallaka har da Manjo-Janar Hossein Salami, Shugaban Rundunar IRGC ta Iran da wasu manyan kwamandoji da manyan masana a tashar Nukiliyar.
Rundunar Tsaron Isra’ila (IDF) ta sanar da cewa jiragen yaki sama da 200 ne suka yi aikin kai hare-haren kuma sun kai su ne a muhimman wurare sama da 100 a Iran.
Sai dai jim kadan bayan labarin kai harin, Iran ta mayar da martani.
Kafofin yada labaran gwamnatin kasar sun rawaito cewa Iran ta harba jirage marasa matuka sama da 100 da suke hakon wurare daban-daban a cikin Isra’ila.
Kazalika, Shugaban addini na kasar, Ayatollah Ali Khomenei ya sha alwashin sai Isra’ila ta dandana kudarta.
Tuni rahotanni daga Isra’ila suka nuna yadda mutane suka shiga sayayya a kasuwanni ba ji ba gani suna adanawa saboda gudun abin da zai faru na martani.
Wasu hotuna da kamfanin dillancin labaran Faransa (AFP) ya wallafa sun nuna tituna a biranen Tel Aviv da Kudus sun dade.
Lamarin dai ya sa an soke tashi da saukar jirage zuwa kasashe da dama na yankin na Gabas ta Tsakiya.