Jihar Gombe na ƙarfafa haƙƙoƙin yara masu nakasa — Ƙungiyar JONAPWD
Published: 20th, February 2025 GMT
Ƙungiyar Masu Nakasa ta ƙasa reshen Jihar Gombe (JONAPWD), ƙarƙashin jagorancin Shugabanta kuma Sakataren Zartarwa na Hukumar Kula da Masu Nakasa ta Jihar, Dokta Isiyaku Adamu.
Ƙungiyar ta shirya taro na musamman tare da iyayen yara da suke fama da matsala irin ta nakasar jiki da kuma ta taɓin hankali.
Wannan taron na musamman, wanda aka gudanar a ofishin JONAPWD da ke Gombe, ya zama wata muhimmiyar dama don tattauna matsaloli, musayar ƙwarewa da kuma ƙarfafa fafutuka don kare haƙƙoƙin yara masu fama da matsala irin ta nakasar jiki da kuma ta taɓin hankali.
A jawabinsa, Dokta Adamu ya bayyana cewa yara masu nakasar jiki da kuma ta taɓin hankali na fuskantar manyan ƙalubale wajen samun ilimi mai inganci, kiwon lafiya mai nagarta da kuma shiga cikin al’umma.
Ya ce, wannan nakasa ta hankali da ta jiki tana nufin yanayi da ke shafar fahimtar ƙwaƙwalwa wajen koyo da hulɗa da jama’a.
Sai dai, Dokta Adamu ya yi nuni da cewa idan aka ba wa waɗannan yara goyon baya mai kyau da fahimta, za su iya bunƙasa basirarsu su yi fice, kuma su bayar da gudummawa mai ma’ana ga ci gaban al’umma.
Dokta Adamu ya kuma yi bayani ga iyaye game da dokar masu nakasa ta Jihar Gombe da Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya rattaba wa hannu kwanan nan. Ya bayyana dokar a matsayin wata gagarumar nasara da za ta tabbatar da kariya, ƙarfafawa da haɗa yara masu nakasa tare da iyalansu cikin al’umma.
Daga cikin muhimman kudurorin taron, akwai ƙarfafa yaƙin wayar da kai don isar da saƙon zuwa ga iyaye da masu kula da yara masu nakasa. Wannan zai taimaka wajen ƙarfafawa al’umma fahimtar baiwa da basirar da yara masu nakasar jiki da kuma ta taɓin hankali ke da ita.
Hakazalika, Dokta Adamu ya nuna godiyarsa ga Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya saboda jajircewarsa wajen inganta rayuwar masu nakasa ta hanyar zartar da dokokin da suka dace.
“Muna matuƙar godiya ga jagorancin gwamna da kuma jajircewarsa wajen tabbatar da rayuwar masu nakasa ta inganta,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya nakasar jiki da kuma ta taɓin hankali yara masu nakasa Dokta Adamu ya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
Daga Usman Muhammad Zaria
Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.
Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.
Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.
Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.
Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen tsaro.
CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.