Jihar Gombe na ƙarfafa haƙƙoƙin yara masu nakasa — Ƙungiyar JONAPWD
Published: 20th, February 2025 GMT
Ƙungiyar Masu Nakasa ta ƙasa reshen Jihar Gombe (JONAPWD), ƙarƙashin jagorancin Shugabanta kuma Sakataren Zartarwa na Hukumar Kula da Masu Nakasa ta Jihar, Dokta Isiyaku Adamu.
Ƙungiyar ta shirya taro na musamman tare da iyayen yara da suke fama da matsala irin ta nakasar jiki da kuma ta taɓin hankali.
Wannan taron na musamman, wanda aka gudanar a ofishin JONAPWD da ke Gombe, ya zama wata muhimmiyar dama don tattauna matsaloli, musayar ƙwarewa da kuma ƙarfafa fafutuka don kare haƙƙoƙin yara masu fama da matsala irin ta nakasar jiki da kuma ta taɓin hankali.
A jawabinsa, Dokta Adamu ya bayyana cewa yara masu nakasar jiki da kuma ta taɓin hankali na fuskantar manyan ƙalubale wajen samun ilimi mai inganci, kiwon lafiya mai nagarta da kuma shiga cikin al’umma.
Ya ce, wannan nakasa ta hankali da ta jiki tana nufin yanayi da ke shafar fahimtar ƙwaƙwalwa wajen koyo da hulɗa da jama’a.
Sai dai, Dokta Adamu ya yi nuni da cewa idan aka ba wa waɗannan yara goyon baya mai kyau da fahimta, za su iya bunƙasa basirarsu su yi fice, kuma su bayar da gudummawa mai ma’ana ga ci gaban al’umma.
Dokta Adamu ya kuma yi bayani ga iyaye game da dokar masu nakasa ta Jihar Gombe da Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya rattaba wa hannu kwanan nan. Ya bayyana dokar a matsayin wata gagarumar nasara da za ta tabbatar da kariya, ƙarfafawa da haɗa yara masu nakasa tare da iyalansu cikin al’umma.
Daga cikin muhimman kudurorin taron, akwai ƙarfafa yaƙin wayar da kai don isar da saƙon zuwa ga iyaye da masu kula da yara masu nakasa. Wannan zai taimaka wajen ƙarfafawa al’umma fahimtar baiwa da basirar da yara masu nakasar jiki da kuma ta taɓin hankali ke da ita.
Hakazalika, Dokta Adamu ya nuna godiyarsa ga Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya saboda jajircewarsa wajen inganta rayuwar masu nakasa ta hanyar zartar da dokokin da suka dace.
“Muna matuƙar godiya ga jagorancin gwamna da kuma jajircewarsa wajen tabbatar da rayuwar masu nakasa ta inganta,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya nakasar jiki da kuma ta taɓin hankali yara masu nakasa Dokta Adamu ya
এছাড়াও পড়ুন:
Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
Rundunar Ƴansandan Nijeriya, tare da haɗin gwuiwar sauran hukumomin tsaro, ta samu nasarar cafke mutane biyu da ake zargi da garkuwa da mutane tare da ceto mutane 11 da aka sace a jihohin Delta da Katsina. Wannan na cikin ƙoƙarin ci gaba da yaƙi da miyagun laifuka a faɗin ƙasa.
A jihar Katsina, an daƙile wani yunƙurin garkuwa da mutane a ranar 8 ga Yuni, 2025, a hanyar Danmusa zuwa Mara Dangeza, inda jami’an haɗin gwuiwa suka yi artabu da ‘yan bindiga. Bayan musayar wuta mai tsanani, jami’an suka tilasta masu laifin guduwa da raunukan harbi tare da kuɓutar da mutum 11 da suka sace ba tare da raunuka ba.
Yanzu-yanzu: Gwamnan Delta Oborevwori Ya Fice Daga PDP Zuwa APC Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye AikinsaA jihar Delta, jami’an CP-Special Assignment sun cafke wani Abubakar Hassan, wanda ake zargin jagoran gungun masu garkuwa da mutane ne da ke aiki a jihohi da dama. Bayan gudanar da bincike, ya jagoranci jami’ai zuwa maboyarsu a dajin Ozoro, inda aka ƙwato bindigogi AK-47 guda biyu da harsasai. Hakanan, wani direba, Obi Ezekiel, ya shiga hannu yayin da aka gano bindiga ƙirar gida da alburusai a motarsa.
Babban Sufeton Ƴansanda na ƙasa, IGP Kayode Egbetokun, ya yaba da ƙwarewa da kwazon jami’an tsaro a waɗannan ayyuka, tare da jan hankali cewa rundunar zata ci gaba da gudanar da irin wadannan farmaki don tabbatar da cewa babu mafaka ga masu aikata laifi a duk faɗin Nijeriya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp