Aminiya:
2025-05-01@06:20:01 GMT

An tsinci gawar ɗan sanda a Otal a Ogun

Published: 16th, February 2025 GMT

An tsinci gawar wani Sufeton ’Yan Sanda, mai suna Haruna Mohammed, a cikin wani ɗakin otal a Jihar Ogun.

Marigayin, wanda ke aiki da Hedikwatar ’Yan Sanda ta Ishashi a Jihar Legas.

NAFDAC ta gano wajen da ake sabunta magungunan da suka lalalce a Abiya Gwamnatin Zamfara ta haramta tarukan siyasa saboda tsaro

Ya je otal ɗin Super G Royal da ke rukunin gidaje naAnthony Uzum tare da wata mata da misalin ƙarfe 1:00 na daren ranar Asabar.

Da misalin ƙarfe 8:52 na safiyar washegari ne, manajar otal ɗin, Deborah Adejobi, ta gano cewar ɗakin da suka kama ba a kulle yake ba.

Lokacin da ta shiga, sai ta tarar da ɗan sandan a kwance babu rai, kuma matar da suka zo tare ba ta cikin ɗakin.

Rahoton ’yan sanda ya bayyana cewa mamallakin otal ɗin, Abiodun Olagunju ne, ya kai rahoto ga hukumomi.

Ya kuma bayyana cewa matar da ta tsere ta je wajen masauƙin baƙi da misalin ƙarfe 6 na safe, inda ta nemi ruwan sha.

An ɗauke gawarsa zuwa ɗakin ajiyar gawa na Life Channel Mortuary da ke Olambe.

Kakakin rundunar ‘yan sandan Ogun, Omolola Odutola, ta tabbatar da faruwar lamarin.

Ta ce da farko ba gano ɗan sanda ba saboda ba a samu katin shaidarsa ba, sai bayan da aka bincika aka gano yana aiki da Hedikwatar ‘Yan Sanda ta Ishashi da ke Legas.

’Yan sanda sun fara neman matar da ta tsere, kuma ana ci gaba da bincike don gano dalilin mutuwarsa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗan Sanda Gawa

এছাড়াও পড়ুন:

NEMA Ta Karɓi ‘Yan Nijeriya 203 Da Suka Maƙale A Libya

Haka kuma wasu hukumomin gwamnati sun taimaka, ciki har da Hukumar ‘Yan Gudun Hijira ta Ƙasa, Hukumar Shige da Fice, Hukumar Tsaro ta DSS, Hukumar Lafiya ta Tashar Jirgin Sama da Rundunar ‘Yansanda.

Mutane biyu daga cikin waɗanda aka dawo da su na fama da matsananciyar rashin lafiya, kuma an garzaya da su asibitin New Ikeja don a duba lafiyarsu.

Bayan an yi musu rijista da ɗaukar bayanan yatsunsu, an mayar da su cibiyar mazauna ‘yan gudun hijira da ke Igando, a Jihar Legas, inda za su samu taimako don ci gaba da rayuwa.

NEMA ta ce wannan wani ɓangare ne na ƙoƙarinta na tallafa wa ‘yan Nijeriya da ke cikin mawuyacin hali a ƙasashen waje da kuma taimaka musu su farfaɗo da rayuwarsu cikin aminci a gida.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Kar A Mika Wuya Ga “Damisar Takarda”
  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • Rawar da Arewa za ta taka a Zaɓen 2027
  • NEMA Ta Karɓi ‘Yan Nijeriya 203 Da Suka Maƙale A Libya
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Ta yi wa saurayinta ƙaryar shekarunta 27 maimakon 47
  • Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno
  • Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano