Hare-Haren Isra’ila Sun Keta Yarjiyar Tsagaita Wuta A Kudancin Kasar Lebanon
Published: 15th, February 2025 GMT
Jiragen Yakin HKI Sun kai hare-hare kan wasu muhimman wurare a kudancin kasar Lebanon, wanda hakan keta yarjeniyar tsagaita wuta a tsakanin kasashen biyu.
Kamafanin dillancin labaran IP na kasar Iran, ya bayyana cewa jiragen yakin HKI sun kai hare-hare a kusa da kogin Litan, Yohmor Al-shaqif da kuma Zoutr Al-sharqiyya, da kuma Deir Siryan, zibqin da Yater.
Gwamnatin HKI ta bayyana cewa ta kai hari ne kan rumbunann ajiyar makamai na kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon.
Duk ntare da tsagaita wuta tsakanin Hizbullah da kuma HKI a ranar 27 ga watan Nuwamban shekarar da ta gabata, bayan watanni 14 da fafatawa, sojojin HKI sun ci gaba da kai hare-hare a cikin kasar Lebanin suna kashesu suna lalata makamasu suna kuma rurrusa gidajensu.
Gwamnatin kasar Lebanon ta shigar da kara a gaban MDD kan kan keta hurumin da HKI yiwa yarjeniyar tsagaita wuta a kasar ta Lebanon amma babu wani abu da ta iya in banda yin allawadai da shi. A ranar 27 ga watan Jenerun da ya gabata, gwamnatin kasar Lebanon ta amince ta tsawaita kasancewar sojojin HKI a kudancin kasar Lebanon.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Lebanon
এছাড়াও পড়ুন:
IRGC : Iran ta kai hare hare wurare a kalla 150 a Isra’ila
Wani babban jami’in sojan Iran ya ce an kai hare-hare a kalla wurare 150 a farmakin ramuwar gayya kan gwamnatin Isra’ila, ciki har da wasu sansanonin soji masu matukar muhimmanci.
Da yake zantawa da gidan talabijin na kasar da sanyin safiyar Asabar, Birgediya Janar Ahmad Vahidi, babban mai ba da shawara ga babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran ya ce, rundunar ta IRGC ta yi nasarar aiwatar da shirinta na Operation True Promise III.
A cewar kwamandan na IRGC, an kuma kai hari kan ma’aikatar harkokin soji da cibiyoyin soji da masana’antu a lokacin da Jamhuriyar Musulunci ta Iran ke daukar fansa.
Daga cikin wadanda harin ya rutsa da su sun hada da Manjo Janar Mohammad Bagheri, babban hafsan hafsoshin sojojin Iran, Birgediya Janar Amir Ali Hajizadeh, shugaban sashin kula da sararin samaniyar IRGC, da Manjo Janar Gholam-Ali Rashid, kwamandan babban shalkwatar Khatam al-Anbiya ta kasar.
Har ila yau, hare-haren sun yi sanadin mutuwar tsoffin masana kimiyyar nukiliya Mohammad-Mehdi Tehranchi, Fereydoun Abbasi, da Dr. Abdol-Hamid Minoucher, tare da fararen hula fiye da 70 da suka hada da yara da mata.
Duk da haka, ya sake nanata cewa wannan babban “kuskure” ne daga bangaren Isra’ila, yana mai gargadin cewa, “Dole ne su jira sakamakon.