HausaTv:
2025-09-17@23:12:52 GMT

Kissoshin Rayuwa : Immam Hassan Dan Ali (a) 17

Published: 15th, February 2025 GMT

17-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa Shirin wanda yake kawo maku kissoshi wadanda suka zo cikin alkur’ani mai girma ko cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin Dastane rastan na shahid Aya. Murtadha muttahhari, ko cikin littafin Mathnawi na maulana jalaluddeen, Rumi, ko kuma cikin wasu littafan.

Da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu.

///… Madalla, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, mun ci gaba da kawo maku sirar Imam Alhassan (s) Jikan manzon All..(s) sannan limami na 2 daga cikin limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All..(s) kuma da na farko ga  Fitima(s) diyar manzon All..(s).

A cikin shirimmu da ya gabata mun yi maganar yadda al-amura suka kasance bayan wafatin manzon All..(s) a madina musamman a masallacin manzon All..(s), inda Khalifa Umar ya hana mutanen fadar cewa manzon All..(s) ya rasu. Kuma har ya kai ga yana masu barazanan zai bugesu da takubin da ke hannunsa.

Sannan mun ji yadda ya sawya sama da kasa, a lokacinda Abubakar ya zo masallacin, ya fadawa mutane a cikin masallacin manzon All..(s) kan cewa manzon All..(s) ya rasu.

Bayan haka, sai suka je Sakifa inda Ansar suke taro, a asirce a tsakaninsu don zaben Sa’adu dan Ubada, a matsayin Khalifa, har’ila yau munji yadda aka kashe Sa’adu dan Ubada din a shekara ta 14 ko15 bayan hijira, amma wadanda suka kashe shi, suka ce, ai aljana ce ta kashe shi, da kibiyoyi biyu a kan kirginsa, kuma suka jefa gawarsa a cikin rijiya.

Sannan munji mai yu wa dalilan da suka sa Ansar sun so su zabi Sa’adu a matsayin Khalifa bayan wafatin manzon All..(s). ba tare da sun shawarci iyalan gidan manzon All..(s) ba. Mun ce mai yuwa suna sun kiyaye mutuncinsu da matsayinsu idan wasu ba iyalan gidan manzon All…ba suka karbi shugabancin al-umma.

Daga karshen mun yi maganar cewa shirin kauda iyalan gidan manzon All..(s) daga matsayin da All..da manzonsa (s) suka basu, an dade da kulla shi, saboda manzon All..Ya sha fadawa Aliyu(a) kan cewa akwai wadanda suke adawa da shi a cikin sahabbansa, amma baza su bayyana masa hakan ba, sai bayan wafatinsa.

Sannan munji cewa shugabannnin juyin mulkin da aka yiwa Amirulmuminin (a) bayan wafatin manzon All..(s), manya manyan kuraishawa ne wadanda Abubakar da Umar tare da taimakon yayansu, kuma matan manzon All..(s) suka shirya, saboda dalilan da muka bayyana.

Har’ila yau idan mun koma kan Ansar, wadanda suka taru a Sakifa don gabatar da Sa’adu dan Ubada a matsayin Khalifa. Zamu ga mcewa, shi Sa’adu, ya na da wadanda suke takara da shi, hatta a cikin Ansar kansu. Da farko akwai dan Amminsa wanda ake kira Bashir dan Sa’ad dan Ubada dan Thaalaba Alhazraji, sai kuma Usaid bin Hudair shugaban kabilar Aus cikin Ansar, suna takara da shi a wannan matsayin da yak enema. Ko kuma suna hasadar sa a kan wannan matsayin, ko wanne daga cikinsu ya na ganin ya cancanci matsayin.

Hakama Uwaim dan Sa’ida al-awsi da kuma da Mu’in dan Adiyyi, abokin kungiyar Abubakar ne, duk da cewa su ma Ansar ne.

Suna abota da shi a rayuwar manzon All..(s). don haka wadannan mutane biyu basa son Sa’adu dan Ubada, ya zama Khalifa, don haka sai suka yi sauri suka je suka fadawa Abubakar kan cewa Ansar, sun gabatar da Sa’adu dan Ubada, zasu yi masa mubaya’a a Sakifa.

A lokacinne Abubakar da Umar da Abu ubaida dan jarra da kuma salam maula Abu Khuzaifa suka sami wannan labarin, sun yi gaggawa suka je Sakifa, sannan abinda ya faru ya faru, har aka yiwa Abubakar Bai’a.

Kafin bai’ar dai, Umar yana son yayi magana, amma ya na magana da fushi, sai Abubakar ya ce masa ya yi shiru, shi zai fara magana.

Sai ya ce:

Mu musu hijira mune wadanda suka rika kowa shiga musulunci. Kuma mun fi kowa nasaba mai kyau, kuma mun fito ne daga gidaje masu Daraja a cikin Kuraishawa, …. Sannan mun fi su kusanci ga manzon All..(s).

Ku ‘yan’uwammu ne, a addinin musulunci, ku masu tarayya da mu ne a cikin wannan addinin,

Kun taimawa masu hijira, kun kuma kun yelwata mana,  All..ya saka maku da Alkhairi. Don haka mune shuwagabanni ku kuma wazirai, wato mataimaka.

Larabawa ba za bi, wani a cikin wannan addini ba sai. wanda ya kasance daga wannan kabilar, wato (kuraishawa).

Kada ku yi jayayya da yan uwanku musu hijira, a kan wannan matsayin, wanda All..ya fafitasu da shi.

Don haka na yarje maku, ku yi mubaya’a ga daya daga cikin wadannan mutane biyu  (ya na Umar Dan Khaddabi, da Abu ubaida dan Jarrah). Karshen maganarsa Kenan.

Don haka idan mun dubi Khudunar Abubkar za mu fitar da dalilan da ya kawo na cancantar Kuraishawa ko Muhajirun da khalifanci.

01-Su ne na farkon musulunta.

02-Su ne dangin manzon All..(s) mafi kusa da shi.

Da farko bai yi Karin bayani a kan dalilansa na farko da na biyu ba.

Na cewa su suka fara Imani da manzon All..(s) ba .

Saboda farkon wanda ya yi Imani, ya karbi kiran manzon All..(s), ya kasance tare da shi a yakar makiyansa, ya kuma kare shi daga sharrin shuwagabannin Kuraishwa, kuma shi dan ammin manzon All..(s), kuma  renonsa, sannan mijin diyarsa toli daya bari a duniya ne, mahaifin jikokin sa (s) biyu ne, kuma kofar ilmimsa ne,  shi ne Amirul muminina Aliyu dan Abitalib (a).

Abubakar ya yi watsi da duk wannan a cikin muhajirun, ko kuraishawa, idan ya na nufin kusanci ne ga manzon All…(s), wa ya fi Aliyu kusanci da shi.

A wasu baitocin da ya Aikawa Mu’awiya dan Abi Sufyan, a lokacinda ya aika masa wasika inda a ciki yake yabon kasa da cewa, ai shi ma kawun muminaine, wato manzon All…(s) ya auri Yarsa Uwar muminai “Ummu Habiba” don haka ita uwar muminaice to shi kuma ya zama Kawun muminai.

Sai Imam Ali (a) ya  ba shi amsa da cewa:

Diyar manzon All..abokiyar zama ta ce (matata ce) Amariyarta ce. Tsokar jikinta ta garwaya da jini da kuma namar jikina.

Kuma Jikokin  Ahmadu (s), Yaya nane daga wajenta.  Wake da rabo irin rabona.?

Ga wanda yake da dukkan wadannan falaloli da kusanci da manzon All..Amma Abubakar ya manta da dukkan wadannan falaloli, ya gabatar da Abu ubaida dan Jarra da kuma Umar Dan Khaddabi, a matsayin khalifofin manzon All..(s) a cikin mujirun .

A wata jayayya da da su, Imam Ali (s) ya na fadawa Abubakar, “sun kawo hujja da itaciya sun bar yayanta”. Ya na nufin itaciya itace Kuraishawa, amma sun mata da yayan itaciyar wato, dangin manzon All..cikin Kuraishawa wato banu Hashim, da kuma zurriyar manzon All..(s)  masu tsarki.

Ko menenen kusancinsu da manzon All..(s) ba su fi yayansa da jikokinsa da yayan amminsa kusa da shi.

A lokacin da manzon All..(s) ya yi wafati ya bar amminsa guda wato Abbas dan Abdul muttalib, amma shi bai dade da musulunta ba, manzon All..(s) ya yi wafati.

 Bai dade a cikin addini ba, don ya mshiga addinin musulunci ne a fatahin Makka a shekarata 8 bayama hijira. Don haka a cikin Banu Hashim babu kamar Aliyu (a). Ya hada dukkan falalolin da suka bashi damar zama Khalifa.

*******************************************

Don haka Aliyu dan Abitalib shi ne shugaban Banu Hashim, dangin manzon All..(s) a lokacin.

Na farko wa ya Sanya Khalifa Abubakar wikilin Kuraishawa don zaben wanda zai shugabancesu?. Sannan idan har ya wakilce su, to akwai wanda ya fi wadanda ya gabatar a matsayin khalifofi a cikin kuraishawa, kuma sune ‘ya’yan manzon All..yayan amminsa(s).

Don haka Imam Ali (s) ya hujjacesu da abinda suka hujjace Ansar da shi a cikin wata kasidan da yi, yana cewa:

Idan da kusanci ne ka hujjace, mai husumarsu. To waninka ne yafi cancanta da al-amuran Annabi(s), ya kuma fika kusa. Idan da shura ce ka mallaki al-amuransu, to ta yaya haka zai kasance, wadanda suka cancanci bada shawara basa nan.

A cikin wani khudubar sa dangane da wannan batun. yana cewa:…Wallahi ni dan’uwansa ne, (yana nufin Manzon All…(s), .. mai jibantar al-amarinsa ne, kuma dan’amminsa ne, kuma magajin ilminsa ne, wa ya cancanci gadonsa fiye da ni.

Hakika mutane sun ki bin Baban Alhasan, sun yi watsi da falalolinsa, da fifikonsa, da wasiyyan annabi (s) dangane da shi. Saboda kodayin shugabanci da khalifanci.

 A lokacinda Abubakar ya kammala khudubarsa, wanda muka gabatar, ya kuma gabatar da Umar da Abu Ubaida dan Jarrah, a matsayin wadanda suka cancanci wannan matsayin a cikin Kuraishawa, ko muhajirun.

Sai Umar yayi sawri ya ce: Hakan zai kasance ka na da ranka (ya Abubakar)?, bai yu wa wani ya kawda kai daga matsayin da manzon All..(A) ya tsaida kai.

A nan sai mu ce: bamu san wani lokaci ne manzon All..(s) ya sanya shi Khalifansa ba!. Abinda muka sani shi ne, kwanaki kafin wafatin sa, manzon All..(s) ya sanya shi cikin rundunar da Usama yake jagoranta. Usama dan Zaidu, dan shekara 17 a duniya, inda manzon All..ya ce ya tafi kasar Roma ya kuma yaki kafirai a can.

Don haka manzon All..(s) ya bar shugaban Usama dan zaidu shugaban Abubakar da Umar ne. Shi ne kwamandan su a yakin.

A cikin wannan halin ne aka yiwa Abubakar Bai’a. Da farko Umar ne ya yi masa bai’a, sannan Bashir dan Ubada, dan uwan Sa’adu dan Ubada, sannan sauran wadanda suke cikin kungiyarsa wadanda suka hada da  Usaid dan Hudair da Awim dan Sa’idah, da Mu’in dan Adiy, da Abu Ubaida dan Jarrah, da Salam maula abu Khuzaifa da Khalid dan walid, wanda ya fi kowa tsanantawa mutane, su yi bai’a wa Abubakar.

Banda haka Umar ya tilastawa wasu yin bai’a ga Abubakar, sannan a lokacinda mutane suke ribibin yi wa Abubakar Bai’a, sai wasunsu sun tattaka Sa’adu dan Ubada don yana kwance a kasa a lokacin saboda rashin lafiya.

Sai ansar suna cewa, an kashe Sa’adu, Sai Umar yace: Ku kashe shi, All..ya la’anci shi, shi ma’abucin fitina ne.

Bayan da aka yi masa Bai’a, sai mutanensa suka sa shi a gaba suna yabonsa suna masa kirari a matsayin Khalifan manzon All..(s), su na masa kamar yadda ake yi wa ‘Amarya’ zuwa gidan mijinta. suka raka shi zuwa masallacin manzon All..(s).

Sun yi haka ne. a lokacin gawar manzon All..(s) mai tsarki, tana kwance a kan gado ba’a kammala yi masa wanka ba da likkafani ba.

Masu sauraro a nan zamu dasa aya sai kuma wata fitowa idan All..ya kaimu wassalamu alaikum wa rahamatullahi wa barakatuhu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: iyalan gidan manzon All a matsayin Khalifa cikin Kuraishawa cikin kuraishawa wannan matsayin bayan wafatin wadanda suka masu sauraro wa Abubakar Abubakar ya

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu

Sojoji biyu sun ji rauni bayan wani harin kwanton baya da ’yan bindiga suka kai kan ayarin motocin Kwamandan kwamandan Rundunar Sojoji ta 382 Ƙaramar Hukumar Faskari ta jihar Katsina.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Ruwan Godiya, kan hanyar Sheme–Kankara, lokacin da tawagar Operation Fansan Yamma (OPFY) ke wucewa.

Ganau sun ce sojojin na kan hanyar ziyartar sansanonin sojoji a yankunan Faskari da Mabai da Ɗan Ali lokacin da aka kai musu hari.

Sai dai sun yi nasarar tunkarar ’yan bindigar har suka kuvuta, kodayake sojoji biyu sun samu raunuka na harbi kuma aka kai su asibitin sojoji domin jinya.

An kai wa sojojin harin ne a rana ɗaya da shugabannin al’ummar Faskari suka zauna da wakilan ’yan bindiga domin rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya.

’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS

Hakan ya sanya Faskari zama ƙaramar hukuma ta baya-bayan nan da ta shiga irin wannan sulhu bayan ƙananan hukumomin Ɗanmusa da Jibia, Batsari da Ƙanƙara, Kurfi da Musawa.

Yarjejeniyar na neman kawo ƙarshen tashin-tashina, garkuwa da mutane da kuma ƙaura da ake fama da su a jihar.

Amma akwai shakku kan ɗorewar ta, domin wasu daga cikin shugabannin ’yan bindigar sun bayyana cewa sulhun ya shafi ƙananan hukumomin da suka shiga yarjejeniyar kawai, lamarin da ya janyo tsoron cewa sauran wuraren da ba su rattaba hannu ba, suna iya ci gaba da fuskantar hare-hare.

Wasu mazauna Ruwan Godiya sun ce ayyukan ’yan bindiga na ƙara ta’azzara a sassan Katsina duk da yarjejeniyar sulhun da aka ƙulla da wasu daga cikin shugabanninsu.

Masana sun bayyana cewa hakan ya nuna raunin irin waɗannan tsare-tsare na sulhu, tare da tabbatar da buƙatar ƙarin sa-ido a yankunan da ke fuskantar barazana.

Sulhun Faskari da ’yan bindiga

Ƙaramar Hukumar Faskari ta zama ta baya-bayan nan a Jihar Katsina da ta shiga yarjejeniyar zaman lafiya da ’yan bindiga, domin kawo ƙarshen kashe-kashe, garkuwa da mutane da kuma ƙaura da ake fama da su a yankin.

Kamar sauran sulhunan da aka kulla a ƙananan hukumomi guda shida, sharuddan yarjejeniyar sun ba wa ’yan bindiga damar shiga garuruwa da kasuwanni da asibitoci.

Haka kuma, za su sako duk wanda aka yi garkuwa da shi ba tare da sharaɗin ba. A sakamakon haka, al’umma za su iya komawa gona da kasuwanni cikin kwanciyar hankali ba tare da fargabar farmaki ba.

Yarjejeniyar ta biyo bayan taron al’umma da aka yi a Faskari, inda fitaccen shugaban ’yan bindiga, Ado Aliero, wanda ake nema ruwa a jallo, ya tabbatar wa manoma tsaronsu.

“Daga yau kowa ya koma gona cikin kwanciyar hankali; ba abin da zai faru a Faskari baki ɗaya,” in ji Aliero cikin wani bidiyo da Aminiya ta gani.

Aliero ya ɗora laifin rushewar yarjejeniyar da aka yi a baya kan cafke ɗansa, yana mai cewa ya bi duk hanyoyin lumana, amma abin ya gagara, kafin ya koma tayar da hankali.

A wani bidiyo daban kuma, wani ɗan bindiga da aka gani sanye da rigar harsashi ya zargi hukumomi da nuna wariya da rashin adalci, yana mai cewa sulhu na gaskiya zai tabbata ne kawai idan aka yi adalci ga kowa.

Sai dai duk da rahotannin da ke cewa jami’an gwamnati da na tsaro sun halarci taron, gwamnatin Jihar Katsina ta nesanta kanta daga wannan yarjejeniyar.

Akwai masu kawo cikas — Gwamna Raɗɗa

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa, ya ce duk da irin ƙalubalen tsaro da ake fuskanta, gwamnatinsa na samun ci-gaba, sai dai akwai masu ƙoƙarin kawo cikas.
Ya bayyana haka ne a wani taron shawarwari da aka gudanar a Katsina ranar Lahadi, wanda ya tattaro manyan masu ruwa da tsaki ciki har da sarakunan gargajiya da shugabannin siyasa da shugabannin tsaro da masana, ’yan kasuwa da shugabannin addini.
Gwamnan ya ce tsaro ne ginshiƙin ajandar ci-gabansa tare da ilimi da noma da kiwon lafiya da kuma tallafa wa ƙanana da matsakaitan ’yan kasuwa.
Ya sanar da cewa gwamnati za ta gina gidaje 152 ga iyalan da aka raba da muhallansu a Jibia, tare da shirya shirin tallafa wa tubabbun ’yan ta’adda da suka domin kada su koma ɓarna.
Haka kuma ya yaba wa jami’an sa-kai da ƙungiyoyin tsaro na gari da suka taimaka wajen dawo da ƙwarin gwiwa a tsakanin jama’a.
Cikin manyan da suka halarci taron akwai tsohon Gwamna Aminu Bello Masari da dattijo Sanata Abu Ibrahim da fitaccen dan kasuwa Alhaji Ɗahiru Mangal da Sarkin Daura Alhaji Faruk Umar Faruk da tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika, Ministan Gidaje Arc. Ahmed Ɗangiwa, da kuma Hadiza Bala Usman mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsare-tsare.
Sauran sun hada da tsohon Daraktan DSS Alhaji Lawal Daura, tsohon Daraktan NIA Ambasada Ahmed Rufai, tsohon Shugaban Kamfanin na NNPC Injiniya Abubakar Yar’adua da Babban Alƙalin jihar Alhaji Musa Ɗanladi, da kuma manyan hafsoshin soja da dama da suka yi ritaya.
Hakazalika, an samu halartar manyan jami’ai, malamai daga jami’o’i da ƙungiyoyin ƙwadago da ƙungiyoyin farar hula da ’yan kasuwa da sauran shugabanni daga sassa daban-daban na jihar.
Gwamna Radda ya jaddada cewa zai ci gaba da karɓar suka da shawarwari daga masu kishin ƙasa, tare da kira ga haɗin kai domin shawo kan matsalolin tsaro da tattalin arziki da jihar ke fama da su.

Abin da mahalarta suka ce

A nasa vangarenm Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina, Faruk Lawal Joɓe, ya bayyana cewa gwamnatin Raɗɗa ta samar da sama da ayyuka 35,903 a fannoni daban-daban ta karkashin manufar “Gina Makomarka.”

Joɓe ya bayyana ce an samar da ayyukan ne ta hanyar ɗaukar malamai da shugabannin unguwanni da jami’an tsaro na sa da mafarauta da sauransu domin su riƙa taka rawa wajen wanzar da zaman lafiya.

Ya kuma yi ƙarin haske kan aikin Sabunta Birane na Katsina State Urban Renewal da ya lashe Naira biliyan 74.9 wanda ya shafi manyan ayyuka a Daura da Funtua da Katsina.

Ayyukan sun haɗa da gina sabuwar hanyar Eastern Bypass mai tsawon kilomita 24, titi mai hannu biyu a cikin Katsina, gyaran tituna a Daura da Funtua, da kuma kammala wasu muhimman hanyoyin karkara.

A nasa jawabin, Kwamishinan Tsaro na Cikin Gida, Dakta Nasir Muazu, ya ce gwamnatin Raɗɗa ta ɗauki matakin rashin tattaunawa da ’yan bindiga.

Ya ce abubuwan da ke haifar da ta’addanci sun haɗa da son zuciya da rikice-rikicen albarkatu da sauyin yanayi, da kuma rashin adalci a cikin al’umma.

Ya ƙara da cewa daga 2011 zuwa 2015 matsalar ta tsaya a ƙananan hukumomi biyar, amma ta bazu zuwa 25 a lokacin tsohon Gwamna Aminu Masari bayan shirin afuwa ya faskara.

Kwamishinan ya bayyana cewa hare-haren soji sun lalata maɓoyar ’yan bindiga da dama, sun buɗe manyan hanyoyi, sannan mutum 628 da suka tsira daga hare-hare sun samu kulawar lafiya a bana.

Ya ce yanzu dakarun Community Watch, masu aikin sa-kai da ’yan banga suna mara baya ga jami’an tsaro da ke amfani da jirage marasa matuƙa da makamai da motocin aiki.

Shugaban Ƙungiyar ƙwadago (TUC) na jihar, Muntari Abdu Ruma, ya gargaɗi gwamnati ta yi taka-tsantsan da yarjejeniyar zaman lafiya da ’yan bindiga lura da yarjejeniyar Kankara ta 2016 da ta gagara.

Haka kuma, shugaban ƙungiyoyin farar hula na jihar, Malam Abdulrahman Abdullahi, ya ce akwai buƙatar ƙarin haɗin kai tsakanin jihohin Arewa maso Yamma wajen yaki da ’yan bindiga. Ya yi nuni da cewa ziyarar da dattawan Katsina suka kai wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu a bisa jagorancin Gwamna Raɗɗa ta fara haifar da sakamako mai kyau a Ƙanƙara da Faskari, amma dole a ci gaba da ayyuka cikin tsari.

A nasa ɓangaren, Sanata Ibrahim Tsauri na jam’iyyar adawa PDP, ya ce taron ya fi karkata wajen bayyana nasarorin gwamnati fiye da ba wa mahalarta dama su yi sharhi.

Duk da haka ya ce idan aka ci gaba da irin waɗannan taruka, za su iya kawo sauyi ga jihar bayan shekaru 15 na ƙalubale.

An ce mahalarta taron sun yi alkawarin mara wa gwamnati baya wajen shawo kan matsalar samari, musamman shaye-shaye da sauran laifuka.

Sauran muhimman shawarwarin sun haɗa da haɗe hanyoyin sadarwa a wuri guda da nufin samun nasarar wannan abu da aka sanya a gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Chadi:  Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa  damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya