Kissoshin Rayuwa : Immam Hassan Dan Ali (a) 17
Published: 15th, February 2025 GMT
17-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa Shirin wanda yake kawo maku kissoshi wadanda suka zo cikin alkur’ani mai girma ko cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin Dastane rastan na shahid Aya. Murtadha muttahhari, ko cikin littafin Mathnawi na maulana jalaluddeen, Rumi, ko kuma cikin wasu littafan.
///… Madalla, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, mun ci gaba da kawo maku sirar Imam Alhassan (s) Jikan manzon All..(s) sannan limami na 2 daga cikin limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All..(s) kuma da na farko ga Fitima(s) diyar manzon All..(s).
A cikin shirimmu da ya gabata mun yi maganar yadda al-amura suka kasance bayan wafatin manzon All..(s) a madina musamman a masallacin manzon All..(s), inda Khalifa Umar ya hana mutanen fadar cewa manzon All..(s) ya rasu. Kuma har ya kai ga yana masu barazanan zai bugesu da takubin da ke hannunsa.
Sannan mun ji yadda ya sawya sama da kasa, a lokacinda Abubakar ya zo masallacin, ya fadawa mutane a cikin masallacin manzon All..(s) kan cewa manzon All..(s) ya rasu.
Bayan haka, sai suka je Sakifa inda Ansar suke taro, a asirce a tsakaninsu don zaben Sa’adu dan Ubada, a matsayin Khalifa, har’ila yau munji yadda aka kashe Sa’adu dan Ubada din a shekara ta 14 ko15 bayan hijira, amma wadanda suka kashe shi, suka ce, ai aljana ce ta kashe shi, da kibiyoyi biyu a kan kirginsa, kuma suka jefa gawarsa a cikin rijiya.
Sannan munji mai yu wa dalilan da suka sa Ansar sun so su zabi Sa’adu a matsayin Khalifa bayan wafatin manzon All..(s). ba tare da sun shawarci iyalan gidan manzon All..(s) ba. Mun ce mai yuwa suna sun kiyaye mutuncinsu da matsayinsu idan wasu ba iyalan gidan manzon All…ba suka karbi shugabancin al-umma.
Daga karshen mun yi maganar cewa shirin kauda iyalan gidan manzon All..(s) daga matsayin da All..da manzonsa (s) suka basu, an dade da kulla shi, saboda manzon All..Ya sha fadawa Aliyu(a) kan cewa akwai wadanda suke adawa da shi a cikin sahabbansa, amma baza su bayyana masa hakan ba, sai bayan wafatinsa.
Sannan munji cewa shugabannnin juyin mulkin da aka yiwa Amirulmuminin (a) bayan wafatin manzon All..(s), manya manyan kuraishawa ne wadanda Abubakar da Umar tare da taimakon yayansu, kuma matan manzon All..(s) suka shirya, saboda dalilan da muka bayyana.
Har’ila yau idan mun koma kan Ansar, wadanda suka taru a Sakifa don gabatar da Sa’adu dan Ubada a matsayin Khalifa. Zamu ga mcewa, shi Sa’adu, ya na da wadanda suke takara da shi, hatta a cikin Ansar kansu. Da farko akwai dan Amminsa wanda ake kira Bashir dan Sa’ad dan Ubada dan Thaalaba Alhazraji, sai kuma Usaid bin Hudair shugaban kabilar Aus cikin Ansar, suna takara da shi a wannan matsayin da yak enema. Ko kuma suna hasadar sa a kan wannan matsayin, ko wanne daga cikinsu ya na ganin ya cancanci matsayin.
Hakama Uwaim dan Sa’ida al-awsi da kuma da Mu’in dan Adiyyi, abokin kungiyar Abubakar ne, duk da cewa su ma Ansar ne.
Suna abota da shi a rayuwar manzon All..(s). don haka wadannan mutane biyu basa son Sa’adu dan Ubada, ya zama Khalifa, don haka sai suka yi sauri suka je suka fadawa Abubakar kan cewa Ansar, sun gabatar da Sa’adu dan Ubada, zasu yi masa mubaya’a a Sakifa.
A lokacinne Abubakar da Umar da Abu ubaida dan jarra da kuma salam maula Abu Khuzaifa suka sami wannan labarin, sun yi gaggawa suka je Sakifa, sannan abinda ya faru ya faru, har aka yiwa Abubakar Bai’a.
Kafin bai’ar dai, Umar yana son yayi magana, amma ya na magana da fushi, sai Abubakar ya ce masa ya yi shiru, shi zai fara magana.
Sai ya ce:
Mu musu hijira mune wadanda suka rika kowa shiga musulunci. Kuma mun fi kowa nasaba mai kyau, kuma mun fito ne daga gidaje masu Daraja a cikin Kuraishawa, …. Sannan mun fi su kusanci ga manzon All..(s).
Ku ‘yan’uwammu ne, a addinin musulunci, ku masu tarayya da mu ne a cikin wannan addinin,
Kun taimawa masu hijira, kun kuma kun yelwata mana, All..ya saka maku da Alkhairi. Don haka mune shuwagabanni ku kuma wazirai, wato mataimaka.
Larabawa ba za bi, wani a cikin wannan addini ba sai. wanda ya kasance daga wannan kabilar, wato (kuraishawa).
Kada ku yi jayayya da yan uwanku musu hijira, a kan wannan matsayin, wanda All..ya fafitasu da shi.
Don haka na yarje maku, ku yi mubaya’a ga daya daga cikin wadannan mutane biyu (ya na Umar Dan Khaddabi, da Abu ubaida dan Jarrah). Karshen maganarsa Kenan.
Don haka idan mun dubi Khudunar Abubkar za mu fitar da dalilan da ya kawo na cancantar Kuraishawa ko Muhajirun da khalifanci.
01-Su ne na farkon musulunta.
02-Su ne dangin manzon All..(s) mafi kusa da shi.
Da farko bai yi Karin bayani a kan dalilansa na farko da na biyu ba.
Na cewa su suka fara Imani da manzon All..(s) ba .
Saboda farkon wanda ya yi Imani, ya karbi kiran manzon All..(s), ya kasance tare da shi a yakar makiyansa, ya kuma kare shi daga sharrin shuwagabannin Kuraishwa, kuma shi dan ammin manzon All..(s), kuma renonsa, sannan mijin diyarsa toli daya bari a duniya ne, mahaifin jikokin sa (s) biyu ne, kuma kofar ilmimsa ne, shi ne Amirul muminina Aliyu dan Abitalib (a).
Abubakar ya yi watsi da duk wannan a cikin muhajirun, ko kuraishawa, idan ya na nufin kusanci ne ga manzon All…(s), wa ya fi Aliyu kusanci da shi.
A wasu baitocin da ya Aikawa Mu’awiya dan Abi Sufyan, a lokacinda ya aika masa wasika inda a ciki yake yabon kasa da cewa, ai shi ma kawun muminaine, wato manzon All…(s) ya auri Yarsa Uwar muminai “Ummu Habiba” don haka ita uwar muminaice to shi kuma ya zama Kawun muminai.
Sai Imam Ali (a) ya ba shi amsa da cewa:
Diyar manzon All..abokiyar zama ta ce (matata ce) Amariyarta ce. Tsokar jikinta ta garwaya da jini da kuma namar jikina.
Kuma Jikokin Ahmadu (s), Yaya nane daga wajenta. Wake da rabo irin rabona.?
Ga wanda yake da dukkan wadannan falaloli da kusanci da manzon All..Amma Abubakar ya manta da dukkan wadannan falaloli, ya gabatar da Abu ubaida dan Jarra da kuma Umar Dan Khaddabi, a matsayin khalifofin manzon All..(s) a cikin mujirun .
A wata jayayya da da su, Imam Ali (s) ya na fadawa Abubakar, “sun kawo hujja da itaciya sun bar yayanta”. Ya na nufin itaciya itace Kuraishawa, amma sun mata da yayan itaciyar wato, dangin manzon All..cikin Kuraishawa wato banu Hashim, da kuma zurriyar manzon All..(s) masu tsarki.
Ko menenen kusancinsu da manzon All..(s) ba su fi yayansa da jikokinsa da yayan amminsa kusa da shi.
A lokacin da manzon All..(s) ya yi wafati ya bar amminsa guda wato Abbas dan Abdul muttalib, amma shi bai dade da musulunta ba, manzon All..(s) ya yi wafati.
Bai dade a cikin addini ba, don ya mshiga addinin musulunci ne a fatahin Makka a shekarata 8 bayama hijira. Don haka a cikin Banu Hashim babu kamar Aliyu (a). Ya hada dukkan falalolin da suka bashi damar zama Khalifa.
*******************************************
Don haka Aliyu dan Abitalib shi ne shugaban Banu Hashim, dangin manzon All..(s) a lokacin.
Na farko wa ya Sanya Khalifa Abubakar wikilin Kuraishawa don zaben wanda zai shugabancesu?. Sannan idan har ya wakilce su, to akwai wanda ya fi wadanda ya gabatar a matsayin khalifofi a cikin kuraishawa, kuma sune ‘ya’yan manzon All..yayan amminsa(s).
Don haka Imam Ali (s) ya hujjacesu da abinda suka hujjace Ansar da shi a cikin wata kasidan da yi, yana cewa:
Idan da kusanci ne ka hujjace, mai husumarsu. To waninka ne yafi cancanta da al-amuran Annabi(s), ya kuma fika kusa. Idan da shura ce ka mallaki al-amuransu, to ta yaya haka zai kasance, wadanda suka cancanci bada shawara basa nan.A cikin wani khudubar sa dangane da wannan batun. yana cewa:…Wallahi ni dan’uwansa ne, (yana nufin Manzon All…(s), .. mai jibantar al-amarinsa ne, kuma dan’amminsa ne, kuma magajin ilminsa ne, wa ya cancanci gadonsa fiye da ni.
Hakika mutane sun ki bin Baban Alhasan, sun yi watsi da falalolinsa, da fifikonsa, da wasiyyan annabi (s) dangane da shi. Saboda kodayin shugabanci da khalifanci.
A lokacinda Abubakar ya kammala khudubarsa, wanda muka gabatar, ya kuma gabatar da Umar da Abu Ubaida dan Jarrah, a matsayin wadanda suka cancanci wannan matsayin a cikin Kuraishawa, ko muhajirun.
Sai Umar yayi sawri ya ce: Hakan zai kasance ka na da ranka (ya Abubakar)?, bai yu wa wani ya kawda kai daga matsayin da manzon All..(A) ya tsaida kai.
A nan sai mu ce: bamu san wani lokaci ne manzon All..(s) ya sanya shi Khalifansa ba!. Abinda muka sani shi ne, kwanaki kafin wafatin sa, manzon All..(s) ya sanya shi cikin rundunar da Usama yake jagoranta. Usama dan Zaidu, dan shekara 17 a duniya, inda manzon All..ya ce ya tafi kasar Roma ya kuma yaki kafirai a can.
Don haka manzon All..(s) ya bar shugaban Usama dan zaidu shugaban Abubakar da Umar ne. Shi ne kwamandan su a yakin.
A cikin wannan halin ne aka yiwa Abubakar Bai’a. Da farko Umar ne ya yi masa bai’a, sannan Bashir dan Ubada, dan uwan Sa’adu dan Ubada, sannan sauran wadanda suke cikin kungiyarsa wadanda suka hada da Usaid dan Hudair da Awim dan Sa’idah, da Mu’in dan Adiy, da Abu Ubaida dan Jarrah, da Salam maula abu Khuzaifa da Khalid dan walid, wanda ya fi kowa tsanantawa mutane, su yi bai’a wa Abubakar.
Banda haka Umar ya tilastawa wasu yin bai’a ga Abubakar, sannan a lokacinda mutane suke ribibin yi wa Abubakar Bai’a, sai wasunsu sun tattaka Sa’adu dan Ubada don yana kwance a kasa a lokacin saboda rashin lafiya.
Sai ansar suna cewa, an kashe Sa’adu, Sai Umar yace: Ku kashe shi, All..ya la’anci shi, shi ma’abucin fitina ne.
Bayan da aka yi masa Bai’a, sai mutanensa suka sa shi a gaba suna yabonsa suna masa kirari a matsayin Khalifan manzon All..(s), su na masa kamar yadda ake yi wa ‘Amarya’ zuwa gidan mijinta. suka raka shi zuwa masallacin manzon All..(s).
Sun yi haka ne. a lokacin gawar manzon All..(s) mai tsarki, tana kwance a kan gado ba’a kammala yi masa wanka ba da likkafani ba.
Masu sauraro a nan zamu dasa aya sai kuma wata fitowa idan All..ya kaimu wassalamu alaikum wa rahamatullahi wa barakatuhu.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: iyalan gidan manzon All a matsayin Khalifa cikin Kuraishawa cikin kuraishawa wannan matsayin bayan wafatin wadanda suka masu sauraro wa Abubakar Abubakar ya
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
Rayukan al’umma gami da dukiya musamman na ababen hawa na ci gaba da salwanta a Mahadar hanya ta yankin Tipper-garage da ke Dutse-Baupma, da ke kan titin da ya tashi daga garin Dutsen-Alhaji ya nufi garin Bwari, a yankin Birnin Tarayya Abuja.
Titin da ke mastayin tagwaye ya haɗa yankin da garin Jere da ke Jihar Kaduna.
Hanyar na ci gaba da ganin ƙaruwar kwararan motoci a sakamakon ingancinta da kuma karancin matsalar tsaro, idan a ka kamanta ta da babban titi Abuja zuwa Kaduna.
Rawar da Arewa za ta taka a Zaɓen 2027 An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifasAdadin motoci da ke bin titin ya kara dagawa a bayabayan nan a dalilin mummunan cunkushewar hanya da ake fuskanta a garin Zuba Abuja da kuma Madalla da ke Jihar Neja, a sakamakon rufe hannu guda na hanyar biyo bayan fara aikinsa da wani sabon kamfani ke yi, bayan karbe aikin daga kamfanin Bega.
Baya ga motoci na matafiya da ke yawan ratsawa ta hanyar, akwai kuma motocin tifa da ke daukar duwatsu daga kamafanonin fasa duwatsu biyu da ke kusa da mahadar hanyan suna kai wa yankuna daban-daban na Abuja dama kewaye.
Aminiya ta ba da labarin cewa hatsarin mota na baya bayan nan da a ka fuskanta a hanyar su ne wanda ya auku a ranar Asabar 5 ga wannan watan na Afrilu, 2025, inda a ka rasa rayukan mutum biyar, bayan wata babbar mota tirela da ta fito ta kusurwan Bwari ta fuskanci matsalar tsinkewar birki a yayin da ta ke gangarowa daga hayin madatsar ruwa na Usuma dam da ke kan titin.
Tirelar ta taka kekunan adaidaita sahu guda biyar da ke daukar fasija a gefen hanayar, baya ga wani adadi na baburan acaba.
Kwana biyu bayan aukuwar hatsarin, an sake fuskantan wani a ranar Litinin da ta biyo baya inda wata babbar mota irin ta daukar bulo da ke dauke da albasa daga wata jiha ta Arewa ta rasa birki a yayin saukowa daga gangarar hanyar.
Ta buge kekunan kafin ta kife a kusa da wani magudanan ruwa da ke jikin hanyar.
An bada labarin rasa mutum biyu a yayin hatsarin, baya ga wasu da su ka tsira da raunuka.
Asarar rayuka da ta dukiya da muka yi — Masu tukin adaidaita sahu
Malam Fahad Musa na cikin shugabannin kungiyar ’yan yuniyon na masu sana’ar tukin Keken Adaidaita sahu da ke aiki a wurin.
Ya ce hatsarin farko ya faru ne da misalign karfe 7 na dare inda ya ce sun rasa mambobinsu uku, sai kuma dan acaba guda, a yayin da mutum na biyar din kuwa ya rasa ransa ne a dalilin harbinsa da bindiga da ake zargin wasu da suka taho cikin ayarin motoci suka yi, kamar yadda majiyoyi daban-daban suka shaidawa Aminiya.
Shugaban na ’yan yuniyon ya shaida wa wakilinmu a yayin ziyara a wajen cewa an kuma rasa kekune biyar a yayin hatsarin bayan motar ta bi ta kansu.
Ya ce faduwar motar ta farko ta yi sanadiyyar rufe hannu guda sannan ba a kai ga cire ta ba sai bayan hatsari na biyu a ranar Litinin.
Ya ce, a lokacin da ake kokarin zakulu mutane da suka mutu da kuma wadanda suka yi raunukan daga karkashin ababan hawan a ranar Asabar, an rufe daukacin tagwayen titin biyu da lamarin ya kai ga jawo takaddama bayan ayarin jami’an tsaro sun bulla ta wajen.
Wani da ya shaidi lamarin, ya shaida wa Aminiya cewa, a lokacin da ayarin motocin suka bullo, wani babba a cikin tawagar ya fito daga cikin mota tare da neman da a bude masu daya hanyar, amma sai ’yan asalin al’ummar yankin suka ki amincewa da bukatar hakan.
Ya kara da cewa, matasan sun bi motocin ayarin da jifa bayan sun kutsa ta daya hanyar da nufin wucewa, kuma a nan ne sai wasu daga cikin jami’an tsaron suka yi harbi cikin iska, a yayin da wani kuma ya harbi daya daga cikin matasa ’yan asalin yankin mai suna Timothy John, da ya mutu nan take.
Bayan nan, ayarin sun wuce da motocinsu cikin hanzari, kamar yadda aka bayyana wa Aminiya.
A yayin zantawarsa da Aminiya shugaban n ’yan yuniyon na masu sana’ar tukin adaidaita sahu ya ce, daya daga cikin direbobinsu mai suna Yusuf Auwal na cikin wadanda harsashin bindiga ya bi ta jikinsa.
Ya ce, bayan nan an garzaya da shi zuwa garinsu inda yake cigaba da jinya a yanzu.
Babban Kwamandan Hukumar Kare Hadurra na FRSC mai kula da yankin Dutsen-Alhaji, Mista Luka Wuna, ya tabbatar da faruwan haduran biyun, da kuma rasa rayukan, a yayin zantawarsa da wakilinmu a kan lamari.
Akwai bukatar ilimantar da direbobin Tifa
Binciken Aminiya ya bayyanan cewa, matsalar da tifofi ke samu ta shanyewar burki a yayin da suka ɗauko kaya kuma suka sukwano gangarar da daga ita sai marabar titin ita ce a mafi yawan lokaci ke haddasa munanan hadurra a wannan mahada.
Da yawan direbobin tifa matasa ne da basu san dokokin tuki ba sannan kuma suna tukin da ganganci tamkar suna tuka kananan motoci.
Don haka mafi yawa ba sa kula da yadda suke shawo wannan gangara ta la’akari da cewa, burkin tifa iska ce.
Wani masanin harkokin sufuri da ba ya son a ambaci sunansa ya ba da shaara cewa, ya kamata hukumomin da abin ya shafa su rinka shirya wa direbobin musamman na Tifa bita kan ka’idojin tuki da alamomin hanaya da kuma hatsarin da ke tattare da burkin mota mai dauke da iska.
Abinda ke jawo hatsari a wajen
Malam Anas Mu’azu na cikin ma’aikatan tattara haraji na Karamar Hukumar Bwari da ke ba da tikiti a wajen.
Ya ce, yawancin direbobi da ke fuskantar hatsarin baki ne da ke bi ta gangaren hanyar ba tare da cikakken masaniya a kan yadda wajen yake ba.
Ya ce, ”wutar ba da umarnin wucewa a wajen da ke da kusurwa 4 na bukatar tsayawar mota na wani lokaci a duk ta inda ta fito saboda dogon layi da motoci ke yi, sannan indan wutar ta haska don wucewa, adadi kadan ne na motoci ke iya wucewa kafin ta sake bukatar tsayar da mota,” in ji shi.
Malam Anas ya kara da cewa yawancin bakin direbobi da ke bin hanyar ba su da masaniya a kan tsarin wutar da kuma yanayin hanyar kasancewar babu allunan alamomi na hanya da ke fadakarwa a kan titin.
Ya ce, haka kuma a baya an cire kunyar kan titi da ke sa motoci rage gudun mota. ”A baya akwai kunyar titi na rage gudun da adadinsu ya kai kamar guda biyar, amma sai a ka cire su a lokaci guda ta hanyan kankare su daga kan hanyar,” in ji shi.
Ya ce, ko da Ministan Birnin Abuja Mista Nyesom Wike ya ba da aikin sake gina hanyar a bayabayan nan, ba a maida kunyar titin ba, har zuwa lokacin da haduran baya-bayan nan su ka auku..
Yadda za a magance matsala —Masu Tifa
Haka kuma Aminiya ta zanta da daya daga shugabannin masu motocin tifa da kuma harkar sayar da duwatsu daga kamfanoni biyu na fasa dutsi da ke yankin mai suna Kwamred Ose Idasho inda ya ba da shawarwaari kan yadda ya ke ganin za a magance yawaitar haduran, da ya ce sun bayar a yayin wani zama na musamman da Jami’an Hukumar Magance Hadurra ta FRSC a yankin.
Ya ce, “abu na farko shi ne bukatar a sa alamomin hanya tun daga kamar kilo mita uku kafin mahadar hanyar da zai rika sanar da direba hatsarin wajen tare da bukatar da ya yi takatsantsan.
“Sai kuma a sa abubuwa da ke sa rage gudun mota na kunyar hanya samfurin roba ba na siminta ba, da zai rika yin kara idan direba ya yi yunkurin yin gudu sosai. Hakan zai kara wa direba karsashi ko da ya fara yin gyangyadi.
“Mun kuma bukaci jami’an na FRSC da nemi dauki daga Hukumar Kula da Gine-gine ta Abuja kan su kawar da wuraren da ke sa mutane na tsayawa ta wurin, tare da mayar da shi sarari, sai kuma samar da wurearen yin lodi da kuma hana yin lodi a gefen titin.
“Haka kuma akwai bukatar a gyara wasu daga cikin fitilun ba da hannu da suka daina yin aiki, kamar wanda ya shiga ta bangaren Bamuko ta inda motocin tifa ke shiga da kuma yawan fita.
Sai kuma uwa-uba a gina gadar sama a wajen da zai rage girman gangarowar motoci da ke fitowa ta kusurwar Bwari ko DutsenAlhaji inda motocin za su bi ta saman gada,” in ji jagoran masu motocin tifa.
Ya kamata a gina gadar sama
Shi ma a zantawarsa da Aminiya, Sakataren Hakimin yankin na Dutse-Baupma mai suna Simon Luka da ya yi bayani a madadin hakiminsu, ya ce, hatsarin motoci a wajen ya jima yana jawo masu fargaba da kuma asarar rayuka da dukiya.
Ya buƙaci Ministan Birnin Tarayya Mista Nyesom Wike da ya taimaka wajen yin aikin gadar sama a wajen don magance matsalar.
Ya ce, tarihin farawar matsalar ba za ta gaza shekara 20 bayan an yi aikin hanyar.
Ya ce, matashin da aka kashe bayan jami’an tsaro sun buɗe wuta a wajen mai suna Timothy John, bai wuce shekara 20 ba kuma lamarin ya faru ne kasa da mako guda bayan mai gidansa ya yaye shi daga aikin walda da ya ke yi, inda yake shirin buɗe na kansa.
Ya kara da cewa, “sai dai har zuwa lokacin ziyarar nan babu wata ta’aziyya ko ta jaje da muka samu daga jamiu’an tsaro ko kuma hukuma, kan mutuwar matashin.”
Aminiya ta tuntubi Babbar Jami’ar Hulda da Jama’a a Sakatariyar da ke Kula da Sufuri a yankin Birnin Tarayya Abuja mai suna Misis Lecita Wogu, inda ta buƙaci lokaci don yin tsokaci a kan lamarin.