Aminiya:
2025-08-02@04:26:02 GMT

HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar Haruna Zago a Kano

Published: 13th, February 2025 GMT

An yi jana’izar fitaccen ɗan siyasar nan kuma Shugaban Hukumar Kwashe Shara na Jihar Kano (REMASAB), Alhaji Ahmadu Haruna Zago, a Ƙofar Kudu da ke Fadar Sarkin Kano.

Haruna Zago, ya rasu a Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano, bayan fama da rashin lafiya.

Sojoji sun doki ’yan sanda kan kama ‘mai laifi’ Miƙa makaman ’yan bindigar Katsina ya bar baya da ƙura

Dubban mutane ne suka halarci jana’izar fitaccen ɗan siyasar, daga ciki har da Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, Jagoran Kwankwasiyya, Rabiu Musa Kwankwaso, Sarkin Kano na 16, Mai Martaba Sanusi Lamido Sanusi.

Sauran jami’an gwamnatin Kano da manyan ’yan kasuwa na daga cikin waɗanda suka halarci jana’izar marigayin.

Ga hotunan yadda jana’izar ta wakana:

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Haruna Zago Kwankwaso Rashin lafiya rasuwa Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

NBRDA Za Ta Hada Gwiwa Da KIRCT Domin Habaka Magunguna Da Yaki Da Cututtuka

Gwamnatin Tarayya ta bayyana aniyar ta na hadin gwiwa da Cibiyar Binciken Cututtuka ta Jihar Kano(KIRCT) a fannonin bincike, samar da rigakafi, habaka magunguna da kuma yaki da cututtuka masu nasaba da zafi (tropical diseases).

Darakta Janar na Hukumar Binciken Harkokin Halittu ta Kasa (NBRDA), Farfesa Abdullahi Mustapha ne ya bayyana hakan yayin wata ziyarar ban girma da ya kai hedikwatar KIRCT  da ke Kano.

Farfesa Mustapha ya ce ziyarar na da nufin karfafa hadin gwiwa tsakanin NBRDA da KIRCT domin magance kalubalen da kasa ke fuskanta ta hanyar binciken zamani.

“A matsayina na shugaba a wata muhimmiyar hukuma da ke da alhakin bincike da ci gaban fasahar halittu a fannonin abinci da noma, lafiya, masana’antu da muhalli, muna da cikakken shiri na tallafa wa KIRCT don cimma manufofinta.”

Ya yaba da kayan aiki na zamani da ke cibiyar, yana mai cewa suna da babban amfani wajen kawo sakamako mai tasiri da kuma daga martabar Najeriya a fagen binciken kimiyya na duniya.

A nasa jawabin, Daraktan Janar na KIRCT, Farfesa Hamisu Salihu, ya bayyana cewa cibiyar na mai da hankali kan muhimman fannoni guda uku da suka hada da taimaka wa manyan masu bincike daga Jami’ar Bayero ta Kano da Jami’ar Northwest, da  horar da sabbin masana bincike, wato masu tasuwa, da kuma kaddamar da wani shirin gwaji na horas da dalibai biyar mafi hazaka daga ajin karshe na sakandare kan ilimin fasahar halittu kafin su shiga jami’a.

Farfesa Hamisu ya jaddada muhimmancin kafafen watsa labarai da kuma Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kano wajen bunkasa fasahar halittu da inganta tattalin arzikin ilimi.

Ya kuma sake nanata kudurin KIRCT na ci gaba da gudanar da bincike mai tasiri da amfani.

Wakiliyar Rediyon Najeriya ta ruwaito  cewa an kafa Kano Independent Research Centre Trust(KIRCT) ne domin gudanar da bincike kan kiwon lafiya da cututtuka masu yaduwa da wadanda ba sa yaduwa, masu matukar muhimmanci ga lafiyar jama’a a Najeriya da ma fadin nahiyar Afirka.

 

Khadijah Aliyu

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • PDP ta mutu murus a Kano — Shugaban NNPP
  • NBRDA Za Ta Hada Gwiwa Da KIRCT Domin Habaka Magunguna Da Yaki Da Cututtuka
  • An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano
  • Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato
  • Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Yadda ’yan bindiga suka tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar da Manufar Sauyin Yanayi