Sojoji Sun Yi Nasara Akan ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Sakkwato.
Published: 13th, February 2025 GMT
Dakarun Operation Fansan Yamma sun dakile ayyukan ta’addanci a jihohin Zamfara da Sokoto daga ranar 1 zuwa 10 ga watan Fabrairun 2025.
A cewar wata sanarwa da kodinetan cibiyar yada labarai na Operation Fansan Yamma Laftanar Kanar, Abubakar Abdullahi ya fitar, ya ce harin ya yi sanadin fatattakar ‘yan ta’adda da dama da suka hada da wasu manyan ‘yan ta’adda.
Ta ce aikin na inganta tsaron rayuka da dukiyoyi a yankin.
Sanarwar ta bayyana cewa, a tsawon wannan lokaci, sojoji sun yi nasarar kashe ‘yan ta’adda da dama da suka hada da sarakuna irin su Kachalla Na Faransa, Dogon Bakkwalo, Auta Gobaje da Dan Mai Dutsi da dai sauransu.
Ya bayyana cewa, an kawar da da yawa daga cikin wadannan mutane a wani kazamin fada da aka yi a kananan hukumomin Shinkafi da Zurmi na jihar Zamfara da kuma karamar hukumar Isa ta jihar Sokoto.
Baya ga kawar da wasu manyan mutane, sojojin sun kai farmaki kan maboyar ‘yan ta’adda, inda ta ce an lalata maboyar ‘yan ta’adda kimanin 40, a cikin yankunan Tungar Fulani, Unguwar Goga, Tudun Gangara, da Gidan Maji.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, wannan gagarumin farmakin na da matukar muhimmanci wajen dakile ayyukan ta’addanci a yankin Arewa maso Yamma.
Sojojin sun kuma samu nasarar kwato tarin makamai da alburusai, wanda zai zama muhimmi wajen hana kai hare-hare.
Sanarwar ta jaddada cewa, Operation Fansan Yamma na ci gaba da jajircewa wajen kawo cikas ga ayyukan ta’addanci a yankin Arewa maso yammacin Najeriya da jihar Neja.
Muna kara jan hankalin jama’a da su ci gaba da bayar da bayanai kan ‘yan ta’addan da ke gudun hijira har da Bello Turji da mukarrabansa.
Rel/Aminu Dalhatu/WABABE
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Sakkwato Tsaro Zamfara yan ta adda
এছাড়াও পড়ুন:
Jirgin soji ya kashe ’yan sa-kai 20 da ke fatattakar ’yan bindiga a Zamfara
Aƙalla mutane 20 ne suka mutu bayan wani hari da jiragen sama na sojojin Najeriya (NAF) ya kai domin fatattakar ’yan bindiga a a Jihar Zamfara.
Jiragen sojin sun kashe wasu ’yan sa-kai bisa kuskure, a yayin da ’yan sa-kan suke ƙoƙarin fatattakar ’yan bindiga da suka kai hari a yankin Mani a Ƙaramar Hukumar Maru.
Jiragen sojin sun kai hare-haren ne domin fatattakar ’yan bindiga da suka kai wa manoma hari a kan babura da rana tsaka.
Mazauna yankin sun ce bayan ’yan bindiga sun sace manoma sama da 50 ne jirgin sojin ya amsa kiran gaggawa, amma aka samu kuskure ya kashe wasu ’yan sa-kai da ke ƙoƙarin fatattakar maharan.
Bom ɗin Boko Haram ya kashe fasinjoji 9 a tashar mota a Borno NAJERIYA A YAU: Mokwa: Tsakanin Taraddadin Rashin Matsuguni Da Jimamin Rashin ’Yan-UwaWani mazaunin yankin ya shaida wa kafar BBC cewa, “Mun sanar da jami’an tsaro bayan harin, amma kawai sai muka ga jirgin ya zo ya kashe ’yan sa-kai na mu.”
Wani mazaunin garin ya ce, a yayin da jama’a ke ƙoƙarin taimaka wa wadanda aka kai wa hari, sai ga wani jirgin saman soji ya iso.
Ya ce, “’Yan bindigar sun tafi da mutane 50, amma yayin da muke ƙoƙarin kai ɗauki, sai muka ga jirgin soji, kuma ya fara harbin mu. Kowa ya gudu neman mafaka,” inda ya ƙara da cewa sun yi kamar matattu ne don su tsira.
Wani mazaunin kuma ya yi kira ga jami’an tsaro da su ƙara yawa, inda ya buƙaci a yankin amma su yi taka-tsantsan yayin gudanar da ayyukan.
Har yanzu sojojin Najeriya ba su ce komai ba game da lamarin.
Idan ba a manta ba, ire-iren wannan harin huskure ya faru a baya a yankin Jihar Zamfara. A watan Janairun 2025, wani harin jirgin saman sojin Najeriya ya kashe mutane 16 bisa kuskure, ciki har da ’yan sa-kai da manoma, a ƙauyen Tungar Kara a Jihar Zamfara, bayan an zaci su ’yan bindiga ne.
Hakazalika, a watan Disambar 2024, wani harin jirgin sama a Jihar Sakkwato ya kashe fararen hula 10 a sakamakon abin da Gwamnan jihar ya bayyana a matsayin harin kuskure kan fararen hula.
A watan Disamban shekarar 2023 wani jirgin soja ya kai irin harin inda ya kashe sama da fararen hula kimanin 100 a wurin taron Mauludi a yankin Tudun Biri da ke Ƙaramar Hukumar Igabi a Jihar Kaduna.