Sojoji Sun Yi Nasara Akan ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Sakkwato.
Published: 13th, February 2025 GMT
Dakarun Operation Fansan Yamma sun dakile ayyukan ta’addanci a jihohin Zamfara da Sokoto daga ranar 1 zuwa 10 ga watan Fabrairun 2025.
A cewar wata sanarwa da kodinetan cibiyar yada labarai na Operation Fansan Yamma Laftanar Kanar, Abubakar Abdullahi ya fitar, ya ce harin ya yi sanadin fatattakar ‘yan ta’adda da dama da suka hada da wasu manyan ‘yan ta’adda.
Ta ce aikin na inganta tsaron rayuka da dukiyoyi a yankin.
Sanarwar ta bayyana cewa, a tsawon wannan lokaci, sojoji sun yi nasarar kashe ‘yan ta’adda da dama da suka hada da sarakuna irin su Kachalla Na Faransa, Dogon Bakkwalo, Auta Gobaje da Dan Mai Dutsi da dai sauransu.
Ya bayyana cewa, an kawar da da yawa daga cikin wadannan mutane a wani kazamin fada da aka yi a kananan hukumomin Shinkafi da Zurmi na jihar Zamfara da kuma karamar hukumar Isa ta jihar Sokoto.
Baya ga kawar da wasu manyan mutane, sojojin sun kai farmaki kan maboyar ‘yan ta’adda, inda ta ce an lalata maboyar ‘yan ta’adda kimanin 40, a cikin yankunan Tungar Fulani, Unguwar Goga, Tudun Gangara, da Gidan Maji.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, wannan gagarumin farmakin na da matukar muhimmanci wajen dakile ayyukan ta’addanci a yankin Arewa maso Yamma.
Sojojin sun kuma samu nasarar kwato tarin makamai da alburusai, wanda zai zama muhimmi wajen hana kai hare-hare.
Sanarwar ta jaddada cewa, Operation Fansan Yamma na ci gaba da jajircewa wajen kawo cikas ga ayyukan ta’addanci a yankin Arewa maso yammacin Najeriya da jihar Neja.
Muna kara jan hankalin jama’a da su ci gaba da bayar da bayanai kan ‘yan ta’addan da ke gudun hijira har da Bello Turji da mukarrabansa.
Rel/Aminu Dalhatu/WABABE
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Sakkwato Tsaro Zamfara yan ta adda
এছাড়াও পড়ুন:
Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara
Yarjejeniyar, a cewar daukacin mahalarta taron, ta nuna wani gagarumin mataki na kawo karshen tashe-tashen hankula, garkuwa da mutane da satar shanu a Arewa maso Yamma, da kuma yankin Arewa.
Yarjejeniyar wacce Mai Maradin Katsina da Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi, da shugaban karamar hukumar, Babangida Abdullahi Kurfi suka shirya, ta gudana ne a dajin Wurma, inda ake fama da rashin tsaro.
Manyan jagororin ‘yan bindigan da suka hada da Alhaji Usman Kachalla Ruga da Sani Muhindinge da Yahaya Sani (Hayyu) da kuma Alhaji Shu’aibu duk sun yi alkawarin tsagaita wuta.
Daga baya suka sako mutanen da suka kama kuma suka bar manoma su koma gonakansu ba tare da wata barazana ba.
Sai dai kasa da wata guda da kulla yarjejeniyar, an tattaro cewa ‘yan bindigar sun sake kai hari a Zamfara inda suka yi awon gaba da masallata da dama.
Wata majiya ta cikin garin, ta shaida cewa, harin ya afku ne a lokacin sallar asuba da misalin karfe 5:30 na safe, inda ‘yan bindigar suka afkawa masallacin, suka kewaye shi, sannan suka tattara masallatan zuwa daji.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp