Aminiya:
2025-08-01@01:23:15 GMT

Na yi nadamar yi wa Tinubu kamfe a 2023 — Ɗan Bilki Kwamanda

Published: 12th, February 2025 GMT

Fitaccen ɗan siyasa kuma jigo a jam’iyyar APC a Jihar Kano, Abdulmajid Ɗan Bilki Kwamanda, ya ce ya yi nadamar mara wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu baya a zaɓen 2023.

Yayin da yake zantawa da Aminiya ta wayar tarho, Kwamanda ya ce Shugaba Tinubu ya watsar da waɗanda suka sha wuya a kansa, duba da halin da ƙasa ke ciki a yanzu.

Yadda na ƙi karɓar cin hancin N5bn a gwamnatin Tinubu – Tsohon Hadimi Zulum ya bai wa sabon Shehun Bama sandar sarauta

Ya bayyana cewa, a duk tsawon rayuwarsa, bai taɓa yin nadamar wani abu kamar yadda ya yi nadamar mara wa Tinubu baya ba.

“Da ciwo, amma dole a faɗi gaskiya. Ni cikakken ɗan jam’iyyar APC ne, amma dole na amince cewa gwamnatin APC ta gaza a wajen ‘yan Najeriya.

“Na sadaukar da lokaci da dukiyata wajen shawo kan mutane su zaɓi jam’iyyar, amma a yau ina nadamar hakan,” in ji shi.

Kwamanda, ya kuma nemi afuwar jama’a, inda ya bayyana cewa abubuwan da ya musu alƙawari a kai za a musu, gwamnatin APC ba ta cika ba.

“’Yan Najeriya na cikin yunwa kuma suna cikin fushi. Ba su da tabbas kan tsaro, kuma mulki ba ya tafiya daidai.

“Yawancin mutane ba sa iya cin abinci sau biyu a rana,” in ji shi.

Ɗan Bilki Kwamanda ya yi ƙaurin suna wajen suka da yin adawa mai zafi a tsakanin abokan hamayyar jam’iyyarsa a Jihar Kano.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗan Bilki Kwamanda Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

 Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta

A jiya Litinin ne dai gwamnatin kasar Holland ta sanar da hana wa minstocin tsaron kasa Itmir Bin Gafir, da na kudi, Bitsirael Smotrich shiga cikinta.

Kasar ta Holland ta zargi wadannan mutanen biyu da cewa suna ingiza sojojin HKI da yi wa Falasdinawa kisan kiyashi da kuma fadada yawan matsugunan ‘yan sahayoniya  a yankunan da aka ce nan ne za a kafa Daular Falasdinawa.

 Haka nan kuma gwamnatin kasar ta Holland ta kira yi jakadan HKI a birnin Hauge domin gargadinsa akan yanayin da ake ciki a Gaza, da cewa babu yadda za a iya ci gaba da jurewa akansa, ko kare dalilin jefa yankin cikin wannan halin.”

Wannan matakin na kasar Holland ya zo ne gabanin wani taro da tarayyar turai za ta yi a yau Talata domin jingine aikin tare da HKI a fagen nazari da bincike na ilimi, saboda ta ki tsagaita wutar yaki a Gaza.

Tun da fari, Fira ministan  kasar Holland Dick Schoof ya wallafa a sharin X cewa;  A yayin taron da kasashen turai za su yi, Kasarsa za ta  yi  matsin lamba akan ganin an dakatar da yarjejeniyar kasuwanci da HKI, haka nan kuma kakaba takunkumai akan shigar da kayanta na kasuwanci zuwa kasuwannin turai.

Fira ministan na kasar Holland ya ce, ya fada wa shugaban HKI Ishaq Herzog wannan matakin da suke son dauka ta hanyar tarayya turai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za a fara yi wa ɗaliban jami’o’i gwajin ƙwaya — Gwamnatin Nijeriya
  • Peter Obi zai lashe jihohin Arewa idan ya koma PDP – Jerry Gana
  • 2027: Ba Mu Kafa Haɗakarmu Don Cika Burin Atiku Ba – ADC
  • ZAMFARA: APC Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Dauki Don Matsalar Tsaro Na Kara Tsananta
  • Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya
  • Remi Tinubu ta ba da tallafin Naira biliyan ɗaya ga waɗanda harin Benuwe ya shafa
  •  Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta