Na yi nadamar yi wa Tinubu kamfe a 2023 — Ɗan Bilki Kwamanda
Published: 12th, February 2025 GMT
Fitaccen ɗan siyasa kuma jigo a jam’iyyar APC a Jihar Kano, Abdulmajid Ɗan Bilki Kwamanda, ya ce ya yi nadamar mara wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu baya a zaɓen 2023.
Yayin da yake zantawa da Aminiya ta wayar tarho, Kwamanda ya ce Shugaba Tinubu ya watsar da waɗanda suka sha wuya a kansa, duba da halin da ƙasa ke ciki a yanzu.
Ya bayyana cewa, a duk tsawon rayuwarsa, bai taɓa yin nadamar wani abu kamar yadda ya yi nadamar mara wa Tinubu baya ba.
“Da ciwo, amma dole a faɗi gaskiya. Ni cikakken ɗan jam’iyyar APC ne, amma dole na amince cewa gwamnatin APC ta gaza a wajen ‘yan Najeriya.
“Na sadaukar da lokaci da dukiyata wajen shawo kan mutane su zaɓi jam’iyyar, amma a yau ina nadamar hakan,” in ji shi.
Kwamanda, ya kuma nemi afuwar jama’a, inda ya bayyana cewa abubuwan da ya musu alƙawari a kai za a musu, gwamnatin APC ba ta cika ba.
“’Yan Najeriya na cikin yunwa kuma suna cikin fushi. Ba su da tabbas kan tsaro, kuma mulki ba ya tafiya daidai.
“Yawancin mutane ba sa iya cin abinci sau biyu a rana,” in ji shi.
Ɗan Bilki Kwamanda ya yi ƙaurin suna wajen suka da yin adawa mai zafi a tsakanin abokan hamayyar jam’iyyarsa a Jihar Kano.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗan Bilki Kwamanda Siyasa
এছাড়াও পড়ুন:
Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP
Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa za ta ci gaba da shirin gudanar da babban taronta wanda za a yi a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamba a Ibadan da ke Jihar Oyo.
Tun da farko, Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta hana jam’iyyar gudanar da taron, inda ta ce PDP ta karya dokokinta na cikin gida.
’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi Kotu ta dakatar da gudanar da babban taron PDPMai shari’a James Omotosho, wanda ya jagoranci shari’ar, ya umarci Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), da kada ta karɓi ko ta wallafa sakamakon taron har sai PDP ta cika dukkanin sharuɗan da doka ta tanada.
Sai dai a cikin wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar da yammacin ranar Juma’a, kakakinta na ƙasa, Debo Ologunagba, ya ce jam’iyyar ba za ta dakatar da shirin gudanar da taron ba.
Ya bayyana hukuncin kotun a matsayin tauye haƙƙin dimokuraɗiyya a Najeriya.
Ologunagba, ya ce hukuncin ba zai hana PDP ci gaba da shirye-shiryenta na zaɓen sabbin shugabanni da za su jagoranci jam’iyyar na tsawon shekaru huɗu masu zuwa ba.
Ya yi nuni da cewa Kotun Ƙoli ta tabbatar da cewa jam’iyyu na da ’yancin tafiyar da harkokinsu na cikin gida.
“PDP na kira ga mambobinta da shugabanni a faɗin ƙasar nan da su kuma ci gaba da shirye-shiryen babban taron jam’iyyar,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa jam’iyyar mai bin doka ce, kuma ta umarci lauyoyinta da su ɗaukaka ƙara game da hukuncin kotun.