Aminiya:
2025-07-29@16:14:05 GMT

Yadda na ƙi karɓar cin hancin N5bn a gwamnatin Tinubu – Tsohon Hadimi

Published: 12th, February 2025 GMT

Tsohon Hadimin Shugaban Ƙasa a fannin Ƙimar Ƙasa da Zamantakewa, Fela Durotoye, ya bayyana yadda ya ƙi karɓar tayin cin hancin Naira biliyan biyar yayin da yake aiki a Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.

Yayin da yake jawabi a wani taro a Abuja, Durotoye ya ce wani jami’i da ya ce shi limamin coci ne, ya matsa masa lamba domin ya ƙara farashin wani shirin horo da gwamnati ta shirya.

Zulum ya bai wa sabon Shehun Bama sandar sarauta Dokokin gyaran haraji sun tsallake karatu na biyu a majalisa

Ya bayyana cewa tawagarsa ta ƙiyasta kuɗin aikin zuwa Naira biliyan 1.3, amma bayan kwana uku, aka ce masa ya gabatar da takardar lissafi zuwa Naira biliyan biyar.

“Sun ce kuɗin da na nema ya yi kaɗan, sun ce za su ƙara shi zuwa Naira biliyan biyu.

“Daga nan ne suka buƙaci na ƙara lissafin zuwa Naira biliyan biyar,” in ji shi.

Lokacin da ya tambayi dalilin ƙarin kuɗin, sai jami’in ya ce masa kada ya damu.

“Ya ce min, ‘Ba wani laifi a ciki. Ka yi wa Najeriya hidima sosai, yanzu lokaci ya yi da Najeriya za ta saka maka da alheri,’” in ji Durotoye.

Ya ce ya ƙi yarda da tayin, kuma don guje wa damunsa, sai ya kashe wayarsa.

Watanni kaɗan bayan haka, ya samu labarin cewa an kama wasu jami’an gwamnati da suka wawure Naira miliyan 426 daga kuɗin wani shirin horo da aka shirya.

Durotoye, ya jaddada cewa gaskiya da ɗa’a ne kaɗai za su taimaka wa mutum gujewa cin hanci a Najeriya.

“Idan muna da kyawawan halaye, ba za a samu cin hanci da rashawa a ƙasarmu ba,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnatin zuwa Naira biliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Ya bayyana halin da aka shiga mara daɗi, inda ya jajanta wa iyalan waɗanda suka mutu da waɗanda suka yi asarar dukiyoyi, yana mai tabbatar da cewa gwamnati za ta tallafa musu wajen sake gina musu gidajen su da sauya muhallinsu.

Fintiri ya kuma soki waɗanda ke yaɗa rahotannin ƙaryar game da lamarin, ba tare da fahimtar ainihin abin da ke faruwa ba, inda ya ce hakan yana da nasaba da tuggun siyasa da son zuciya.

Ya bayyana cewa maƙasudin ambaliyar sun haɗa da ruwan sama mai yawa da toshewar hanyoyin ruwa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Remi Tinubu ta ba da tallafin Naira biliyan ɗaya ga waɗanda harin Benuwe ya shafa
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
  • Gwamna Namadi Ya Biya Sama Da Naira Biliyan Daya Ga Tsofaffin Ma’aikata
  • Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutumin Da Ake Tuhuma Da Safarar Miyagun Kwayoyi
  • Arewa za ta kayar da Tinubu a zaɓen 2027 —Babachir
  • Matsalar Lantarki: Ga tsada ga rashin wuta
  • HOTUNA: Yadda Aisha ta koma gidan Buhari na Kaduna
  • Gwamnatin APC ta jefa ’yan Najeriya cikin ƙangin talauci — Shugabar LP
  • ADC ce kaɗai za ta iya magance matsalolin Arewa — David Mark