Iraniyawa mazauna kasar Burkina Faso sun gudanar da bukukuwan murnar cika shekaru 46 da samun nasarar juyin juya halin Musulunci a birnin Ouagadougou.

A wannan karon, kasashen biyu sun daukaka kyakkyawar dangantakarsu da aka gina a shekarar 1984.  

Jakadan Jamhuriyar Musulunci ta Iran a birnin Ouagadougou, Mojtaba Faghihi, wanda ya halarci bikin, ya bayyana cewa juyin juya halin Musulunci a Iran a shekara ta 1979 ya ba da damar “yantar da mu daga tsoma bakin siyasa na kasashen waje da wawashe dukiyarmu”.

A cewarsa, Iran ta samu nasarar dakile makircin makiya da kuma wuce gona da iri na sojojin kasashen waje, da takunkumi da kuma ta’addanci.

A nasa bangaren, ministan harkokin wajen kasar Burkina Faso, Karamoko Jean-Marie Traoré, ya bayyana jin dadinsa da raba wannan lokaci karkashin alamar abota da hadin kai tsakanin al’ummomin kasashen biyu, wadanda suka yanke shawarar tafiya tare tun daga shekarar 1984.

Ya kuma mika sakon shugaban Burkina Faso Kyaftin Ibrahim Traoré, na taya murna dangane da cika shekaru 46 da samun nasarar juyin juya halin Musulunci.

A cewarsa, Iran ita ma kasa ce “da za mu iya koyo daga gare ta, musamman daga juriyarta, hazaka da jaruntaka”.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Bikin hada-hadar ba da hidima na Sin wato CIFTIS na bana da ya kare a jiya a nan Beijing ya jawo hankalin kasashe da kungiyoyin kasa da kasa 85 da suka gudanar da baje koli da tarurruka, kusan kamfanoni 500, ciki hadda wasu daga cikin manyan kamfanoni 500 dake sahun gaba a duniya da manyan kamfanoni masu jagorantar bangarorinsu, sun halarci bikin, kuma an cimma nasara a fannoni sama da 900. A yayin da duniya ke fuskantar rashin tabbas, bikin CIFTIS ya karfafa mu’amala da kuma samun riba da juna.

Alkaluma na nuna cewa, a shekara ta 2024, jimillar cinikin ba da hidima na Sin ya fara wuce dala tiriliyan 1 a karon farko, wanda ya zama sabon tarihi, kuma ya kasance na biyu a duniya.

Masu zuba jari na waje suna kara zuba jari a Sin saboda babbar kasuwa. A halin yanzu, Sin ta zama abokiyar ciniki ta uku mafi girma a kasashe da yankuna 157, kuma ita ce kasa ta farko a fannin cinikin kayayyaki da ta biyu a fannin cinikin ba da hidima a duniya. A gun bikin na wannan shekara, Sin ta sanar da matakai da yawa, ciki har da “hanzarta aikin gwaji a yankunan gwajin ciniki cikin ’yanci da kuma yankunan ba da misali kan ayyukan ba da hidima na kasa” da “gaggauta bude kasuwar hada-hadar ba da hidima”. Wannan ya samu karbuwa sosai a wajen kamfanonin kasashen waje.

Ta hanyar tarurrukan baje kolin, duniya ba kawai ta ga sabbin abubuwa na tattalin arzikin Sin ba, har ma ta fahimci azamar Sin na hadin gwiwa da duniya da gina tattalin arzikin duniya mai bude kofa cikin hadin gwiwa. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  •   Iran Ta Yi Nasarar Gwajin Tauraron Dan’adam ” Nahid 2″ Da Zai Samar Wa Yankunan Karkara Hanyar Sadarwa Ta “Internet”
  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
  • Iran da Saudiyya sun bukaci hadin Musulmi game da halin da ake ci a yankin
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Ministan Tsaron Kasar venezuela Ya Gargadi Amurka Dangane Da Kokarin Juyin Mulki A Kasar
  • Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
  • Burkina Faso: Masu Ikirarin Jihadi Sun Kashe Fararen Hula 50 A Cikin Watanni Hudu
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato