Gwamnatin Kano za ta kafa hukumar kula da masu buƙata ta musamman
Published: 11th, February 2025 GMT
Gwamnatin Kano ta bayyana aniyarta na kafa Hukumar Kula da Masu Buƙata ta Musamman a wani mataki na tabbatar da adalci a tsakanin al’ummar jihar.
Kwamishiniyar Mata da Yara masu bukata ta musamman, wacce Daraktar Jin Daɗi ta ma’aikatar, Binta Muhammad Yakasai, ta wakilta, ta bayyana hakan yayin wani taron tattaunawa na yini guda da masu ruwa da tsaki kan kafa Hukumar Kula da Mutanen da ke da Bukatu na Musamman (PWDs) a Jihar Kano.
Tana jaddada aniyar gwamnati na ƙarfafa PWDs, Yakasai ta ce, “Wannan taro ba kawai haɗuwar ra’ayoyi ba ne, amma wani mataki ne na tabbatar da adalci, haɗawa da ƙarfafa wani muhimmin ɓangare na al’ummarmu.”
Ta bayyana manyan dalilai guda biyar da ke nuna bukatar kafa hukumar PWDs a Kano, waɗanda suka haɗa da kare Haƙƙoƙin PWDs – hukumar za ta kasance mai sa ido don tabbatar da an kiyaye haƙƙoƙinsu da kuma magance wariya.
Sauran sun hada da kirkira da aiwatar da tsare-tsare, inganta samun sauƙin shige da fice, karfafawa da gina kwarewa da haɗin gwiwa da masu ruwa da tsaki.
Yayin da tattaunawa ke ci gaba, masu ruwa da tsaki sun buƙaci a daina tsaya kan dokoki da manufofi kawai, a mayar da hankali kan tasirin su ga rayuwar jama’a.
“Wannan ba kyauta ba ce, buƙata ce. Kafa wannan hukuma al’amari ne na adalci, mutunci, da daidaiton haƙƙi. Mu haɗa kai don ganin ta tabbata,” in ji Yakasai.
Wannan taro, wanda Giving Promise, ƙwararre a shugabanci da haɗin gwiwar matasa a VSO Nigeria, ya shirya, ya bayar da damar tattaunawa kan gaggawar buƙatar samar da hukuma da za ta kula da matsalolin da PWDs ke fuskanta.
Promise ya jaddada muhimmancin hukumar wajen tabbatar da tsare-tsare da suka dace da PWDs a Kano.
“Gwamnati dole ta haɗa kowa a ci gaban jiharmu. Barin PWDs a baya yana hana cigaba. Manufofin SDGs (Sustainable Development Goals) sun jaddada buƙatar kada a bar kowa a baya, kuma kafa wannan hukuma wani mataki ne na tabbatar da cewa PWDs ba wai kawai an haɗa su ba, har ma suna da tasiri a cikin manufofin da suka shafe su,” in ji shi.
Ya bayyana manyan matsalolin PWDs guda biyu da suka haɗa da ƙarancin damar shiga da buƙatar tsarin haɗin gwiwa na musamman.
Ya ce kowane rukuni na PWDs yana da bukatunsa na musamman, kuma ba tare da hukuma ba, za su ci gaba da fuskantar ƙalubale.
“Idan har Kano na son ci gaba, dole a bai wa kowane ɗan ƙasa dama don bayar da gudunmawa. Kafa wannan hukuma ba kawai buƙata ba ce, wajibi ne,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hukumar Kula da Masu Buƙata ta Musamman Jihar Kano kafa hukumar tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
Gwamnatin Kano ta raba kayayyakin aiki na zamani na kimanin Naira Miliyan 250 ga cibiyoyin horas da sana’o’in hannu biyu da ke Kofar Mata da Gwale, domin yaƙi da shan miyagun kwayoyi da aikata laifuffuka a tsakanin matasa, ta hanyar samar da aikin yi.
Kwamishinan Kimiyya da Fasaha, Dakta Yusuf Kofarmata, ya ce an amince da tallafin ne bisa umarnin Gwamna Abba Kabir Yusuf don bunƙasa tsare-tsaren ƙarfafa matasa a jihar.
Ya bayyana cewa an samar da injinan sarrafa fata guda 26 domin cibiyoyin wadanda al’ummar yankunan suka kafa, amma ba su da isassun kayayyakin aiki.
Ya ce Gwamna Yusuf ne ya gina Cibiyar Horaswar ta Gwale kasancewar nan ce mazabarsa, yayin da Dakta Yakubu Adam ya taka rawa wajen gina ta Kofar-Mata.
Ya ce cibiyoyin za su samar da daruruwan ayyukan yi tare da rage matsalolin zaman kashe-wando da ta’addanci a tsakanin matasa.
A nasa jawabin, Ali Musa Kofar-Mata na ƙungiyar IKMA ya gode wa gwamnati bisa wannan gudummawar da ya kira mai sauya rayuwa.
Ya ce cibiyar ta fara ɗaukar matasa maza da mata, kuma horon zai ɗauki watanni uku kafin a shiga sabon zagaye.
Abdullahi Jalaluddeen