Aminiya:
2025-11-03@09:58:30 GMT

Gwamnatin Kano za ta kafa hukumar kula da masu buƙata ta musamman

Published: 11th, February 2025 GMT

Gwamnatin Kano ta bayyana aniyarta na kafa Hukumar Kula da Masu Buƙata ta Musamman a wani mataki na tabbatar da adalci a tsakanin al’ummar jihar.

Kwamishiniyar Mata da Yara masu bukata ta musamman, wacce Daraktar Jin Daɗi ta ma’aikatar, Binta Muhammad Yakasai, ta wakilta, ta bayyana hakan yayin wani taron tattaunawa na yini guda da masu ruwa da tsaki kan kafa Hukumar Kula da Mutanen da ke da Bukatu na Musamman (PWDs) a Jihar Kano.

Tana jaddada aniyar gwamnati na ƙarfafa PWDs, Yakasai ta ce, “Wannan taro ba kawai haɗuwar ra’ayoyi ba ne, amma wani mataki ne na tabbatar da adalci, haɗawa da ƙarfafa wani muhimmin ɓangare na al’ummarmu.”

Ta bayyana manyan dalilai guda biyar da ke nuna bukatar kafa hukumar PWDs a Kano, waɗanda suka haɗa da kare Haƙƙoƙin PWDs – hukumar za ta kasance mai sa ido don tabbatar da an kiyaye haƙƙoƙinsu da kuma magance wariya.

Sauran sun hada da kirkira da aiwatar da tsare-tsare, inganta samun sauƙin shige da fice, karfafawa da gina kwarewa da haɗin gwiwa da masu ruwa da tsaki.

Yayin da tattaunawa ke ci gaba, masu ruwa da tsaki sun buƙaci a daina tsaya kan dokoki da manufofi kawai, a mayar da hankali kan tasirin su ga rayuwar jama’a.

“Wannan ba kyauta ba ce, buƙata ce. Kafa wannan hukuma al’amari ne na adalci, mutunci, da daidaiton haƙƙi. Mu haɗa kai don ganin ta tabbata,” in ji Yakasai.

Wannan taro, wanda Giving Promise, ƙwararre a shugabanci da haɗin gwiwar matasa a VSO Nigeria, ya shirya, ya bayar da damar tattaunawa kan gaggawar buƙatar samar da hukuma da za ta kula da matsalolin da PWDs ke fuskanta.

Promise ya jaddada muhimmancin hukumar wajen tabbatar da tsare-tsare da suka dace da PWDs a Kano.

“Gwamnati dole ta haɗa kowa a ci gaban jiharmu. Barin PWDs a baya yana hana cigaba. Manufofin SDGs (Sustainable Development Goals) sun jaddada buƙatar kada a bar kowa a baya, kuma kafa wannan hukuma wani mataki ne na tabbatar da cewa PWDs ba wai kawai an haɗa su ba, har ma suna da tasiri a cikin manufofin da suka shafe su,” in ji shi.

Ya bayyana manyan matsalolin PWDs guda biyu da suka haɗa da ƙarancin damar shiga da buƙatar tsarin haɗin gwiwa na musamman.

Ya ce kowane rukuni na PWDs yana da bukatunsa na musamman, kuma ba tare da hukuma ba, za su ci gaba da fuskantar ƙalubale.

“Idan har Kano na son ci gaba, dole a bai wa kowane ɗan ƙasa dama don bayar da gudunmawa. Kafa wannan hukuma ba kawai buƙata ba ce, wajibi ne,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hukumar Kula da Masu Buƙata ta Musamman Jihar Kano kafa hukumar tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai

Gwamnatin Jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin fara amfani da ma’adinan ƙarƙashin ƙasa da Allah SWT ya hore ma ta da nufin haɓaka tattalin arzikinta tare da samarwa al’umma aikin yi.

A yayin ƙaddamar da taron masu ruwa da tsaki na Jihar da aka yi a babban ɗakin taron gidan gwamnatin Jihar da ke Damaturu, Gwamnan Jihar Mai Mala Buni ya ce kamfanin haɓaka ma’adanai ta Yobe Limited ita ce kawai hukumar da aka bai wa izini don gudanar da duk ayyukan bincike da haƙar ma’adinai a faɗin jihar.

Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA

Yana mai cewa, kamfanin haƙar ma’adinai na Yobe a halin yanzu shi ne, ƙashin bayan da zai samarwa Jihar hanyoyin dogaro.

“Jihar Yobe tana da wadataccen albarkatun ma’adinai kamar: Limestone, gypsum, kaolin, granite, Quartz, silica da sauran su duk da haka, tsawon shekaru da yawa, waɗannan ma’adinai sun kasance ba a amfani da su sosai kuma a yanzu lokaci ya yi da za a mayar da waɗannan ma’adinai da aka ɓoye zuwa kadarorin da za su samar da ayyukan yi, samar da wadata da kuma ciyar da ci gaban zamantakewa da tattalin arziki na mutanenmu gaba ɗaya.”

“Manufarmu ita ce tsara wani tsari don ci gaban fannin haƙar ma’adinai a Jihar Yobe ta hanyar da ta dace da manufofin Gwamnatin Tarayya na tabbatar da haɗa kan al’umma, jawo hankalin masu zuba jari masu aminci da kuma tabbatar da alhakin gyara muhalli.

“kuma mun yi imanin cewa haƙar ma’adinai idan aka sarrafa shi yadda ya kamata, zai iya zama babban abin da ke haifar da juriyar tattalin arzikin jiharmu, samar da aikin yi ga matasa da kuma samar da kuɗaɗen shiga.”

“Muna hasashen samar da fannin haƙar ma’adinai wanda zai iya aiki a cikin tsarin dokoki, wanda ke tabbatar da ɗorewar muhalli da fa’idar al’umma; wanda ke haɗaka da haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu waɗanda aka amince da riƙon amana; wanda ke jawo hankalin masu zuba jari na ƙasashen waje.” Cewar Gwamna Buni.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
  • Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m