Aminiya:
2025-11-03@12:28:11 GMT

BUA ya raba wa asibitoci magunguna a Sakkwato

Published: 11th, February 2025 GMT

Kamfanin Siminti na BUA ya raba magungunan cututtuka daban-daban na kimanin naira miliyan 35 a ƙananan asibitoci da ɗakin shan magani 16 da ke cikin Ƙaramar Hukumar Wamakko a Sakkwato.

Daraktan Kamfanin BUA, Injiniya Yusuf Halliru Binji, a wurin rabon tallafin maganin ya ce BUA ya ba da tallafi ga asibitoci da ɗakunan shan magani 16 a tsarin da yake da shi na sadaukarwa ga al’ummar da suke kusa da shi, a kowace shekara akan bayar da magani don saukaka samun magani ga jama’ar.

Binji ta hannun Alhaji Sada Suleiman da ya wakilce shi ya ce kamfanin BUA a tsarinsa na rama alheri ya ɗauki wannan da muhimmanci domin ƙarfafa dangantaka.

“Babu tantama dole mu bayyana farin ciki ga irin goyon baya da haɗin kai da muke samu ga jama’a tsawon lokaci.

“Nasarar da kamfanin yake samu tana da alaƙa da haɗin kan jama’ar da ake makwabtaka da su. Saboda haka za mu ci gaba da kula da bunƙasa rayuwar jama’a

“Nan gaba kaɗan za mu ƙaddamar da rijiyoyin burtsatse guda 7 masu amfani da hasken rana a faɗin Sakkwato, bayan raba tufafin makarantar firamari biyar da za a yi ga mutanen yankin.

Daraktan ya gargaɗi waɗanda suka samu tallafin a kan kar su sayar da magungunan domin kyauta ne ga kowa.

Ya ce kamfanin zai haɗa kai da gwamnati don tabbatar da waɗanda aka yi don su sun amfana.

Wasu daga cikin asibitocin da aka yi rabon magungunan sun haɗa da Asibitin garin Bakin Kudu da Gidan Bailu da Kalambaina da Sabon Garin Alu da Gidan Boka da Asare da Arkilla da Guiwa da sauransu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Sakkwato

এছাড়াও পড়ুন:

Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Yabawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Hanyoyi A Fadin Jihar

Daga Usman Mohammed Zaria

Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu, Injiniya (Dr.) Muhammad Uba, ya yaba wa Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, bisa amincewa da sabbin ayyukan gina hanyoyi a fadin jihar, ciki har da na Birnin Kudu.

Ya ce wannan mataki na cikin ajandar gwamnati 12, musamman wajen inganta ci gaban ababen more rayuwa.

A cewarsa, Birnin Kudu za ta amfana da gina hanyoyi masu tsawon kilomita 113, wanda ya hada da hanyoyin kauyuka da wadanda ke hada al’umma da sauran sassan jihar.

Dr. Uba ya bayyana aikin a matsayin babban ci gaba wajen saukaka zirga-zirga, inganta harkokin tattalin arziki da samun sauki ga muhimman ayyuka ga jama’a.

Ya bayyana tabbacin cewa za a dade ana cin moriyar aikin hanyoyin,  tare da hanzar ayyukan ci gaba da bunkasar karamar hukumar.

Shugaban ya yi addu’ar dorewar zaman lafiya da cigaba a Birnin Kudu tare da yin alkawarin ci gaba da hada kai da gwamnatin jiha domin tabbatar da cewa jama’a suna amfana da fa’idodin dimokuraɗiyya.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Uwargidan Gwamnan  Zamfara Ta Yaba Wa  Karamar Hukumar Gusau Bisa Shirin Tallafawa Jama’a
  • Marasa Lafiya A Nasarawa Sun Koka Game Da Yajin Aikin Likitoci
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Yabawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Hanyoyi A Fadin Jihar
  • Yadda matata ta ɓace a Abuja aka tsince ta a Sakkwato
  • Ministar Jin Dadin Jama’a ta Sudan: Mayakan RSF Sun Kashe Mata 300 Da Yi Wa 25 Fyade A El Fasher
  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m