An ce, tsakanin shekarar 2000 zuwa 2023, kasar Sin ta samar da rance da yawansa ya kai kimanin dalar Amurka biliyan 43 ga kasashen Afirka, don su raya bangaren samar da wutar lantarki. Kana a shekarun nan, kamfanonin kasar Sin sun gudanar da dimbin ayyukan samar da wutar lantarki a nahiyar Afirka, kamarsu madatsar ruwa ta Souapiti ta kasar Guinea, da madatsar ruwa ta Djibloho dake kasar Guinea Bissau, da dai sauransu.

Gaba daya an gudanar da ayyukan a kasashe da yankuna fiye da 40 na nahiyar, wadanda suka kara samar da wutar lantarki na kilowatt miliyan 120, da karin layin wutar lantarki mai tsawon kilomita dubu 66. Har ila yau, kasar Sin ta sanar da shirin gina wasu manyan ayyukan samar da wutar lantarki ta hanya mai tsbta guda 30 a nahiyar Afirka, cikin shekaru 3 masu zuwa, a taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka da ya gudana a bara.

Na biyu shi ne, fasahohin Sin a fannin zamanantarwar bangaren samar da wutar latarki suna da amfani ga kasashen Afirka a kokarinsu na raya kasa.

Kasar Sin ta kafa tsarin samar da wutar lantarki mai tsabta mafi girma a duniya, inda fitattun fasahohi da ta samu suka zamo masu rahusa kuma suka dace da yanayin da kasashen Afirka ke ciki. Kana kamfanonin kasar da suke taka muhimmiyar rawa a duniya a fannin sauya salon samar da makamashi mai tsabta, su ma za su iya taimaka wa kasashen Afirka kafa masana’antun hada injunan samar da wutar lantarki.

Na uku shi ne, Sin da Afirka sun cimma matsaya daya a fannin zamanantar da kasa ta hanya mai tsabta. A wajen taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka da ya gudana a bara, Sin da Afirka sun daddale yarjeniyoyi a bangarorin kara yin amfani da makamashi da ake sabuntawa a Afirka, da karfafa hadin gwiwar bangarorin samar da sabbin makamashi, da kara kaimi ga zamanantarwar tsarin kula da aikin makamashi na Afirka, da dai sauransu, wadanda suka nuna ra’ayi daya da kasashen Afirka da Sin suka samu a fannin manufar raya kasa. Hakan ya zo daidai da maganar da Cliff Mboya, masani dake aiki a cibiyar nazarin huldar Afirka da Sin ta kasar Ghana, ya fada, wato “Kasar Sin na kokarin daidaita manufofinta don neman dacewa da Ajandar shekarar 2063 da kungiyar kasashen Afirka AU ta gabatar”. (Bello Wang)

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: samar da wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje

Shugaban kasar Iran ya nuna murnarsa da yin maraba lalai da masu zuba hannun jari daga kasashen waje a Iran

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana Iran a matsayin dandalin da ta dace wajen zuba hannun jari da gudanar da harkar kasuwanci, yana maraba da masu zuba hannun jari na kasashen waje da ‘yan kasuwa na duniya da su shiga harkokin tattalin arziki da zuba hannun jari a Iran.

A yayin bikin bude baje koli karo na bakwai na baje kolin kayayyakin da Iran ke fitarwa zuwa kasashen ketare (Iran Expo 2025) a safiyar yau Litinin, shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yi maraba da baki na kasashen waje da suka halarci wannan baje kolin, yana mai cewa, “Ko da yake ana gabatar musu da wani hoto na daban da ya yi hannun riga da hakikanin Iran da al’ummar kasarta a ketare, amma Iran kasa ce mai karbar baki, kuma al’ummarta masu tausayi da nuna jin kai.”

Yana mai jaddada cewa: Iran wata kafa ce da ta dace da zuba hannun jarin kasuwanci da yawon bude ido na ketare, Pezeshkian ya bayyana cewa da wannan karfin, kuma ta hanyar ciniki, zuba hannun jari, da hadin gwiwa, za a iya samar da makoma mai haske ga duniya, mai cike da tsaro da zaman lafiya.

Ya kuma yi nuni da cewa: Yake-yaken da suka gani a duniya sun samo asali ne sakamakon rashin mutunta hakkokin bil’adama da na kasashe, Pezeshkian ya jaddada mutunta yankin kasar Iran da hakkokin kasashe, yana mai bayyana Shirin Iran na gudanar da duk wani hadin gwiwa a fannin kimiyya, tattalin arziki, siyasa, da zamantakewa da duniya, da kuma mika ilimi ga sauran kasashe ba tare da iyakancewa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar
  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da Portugal
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje
  • Ɗaukewar wutar lantarki ta tsayar da al’amura a Sifaniya da Portugal
  • Sin Za Ta Aiwatar Da Matakan Daidaita Samar Da Guraben Ayyukan Yi Da Raya Tattalin Arziki
  • Rasha ta ayyana tsagaita wuta ita kaɗai a yakinta da Ukraine